New Post

Tuesday, 9 May 2017

'YAR MAFIYA.. 12

�� *'YAR MAFIYA....*��

*Rash Kardam*
        *Sanah S Matazu*
*N. W. A*
Page
*12*
Kafin Yasiraht ta fita har ya tako yazo ida take hannu ya mik'o mata bata iya yin masa musu ba sai ta kama hannu al'amarin da ya ba ma kowa nacikin gurin mamaki, sai da ya janyota k'usa da shi yana kallon kwayar idonta suna iya jin numfashin juna Samar ya kasa d'auke idonsa gada gareta itama haka duk sun shagala da kalon junansu kalon mai d'auke da sak'onni kala-kala a cikinta.

Najwa da ta tsaya zuciyarta na matuk'ar tafarfasa wannan wani irin abu Samar keyi ma Yasiraht duk irin abunda nake masa ai yaci ya gane irin k'aunar da nake masa amma ko sassauta murya bai tab'a min ba irin yanda yayi ma Yasiraht yau tabbas dole na d'au mataki bazai yiwu ta shiga zuciyar da na dad'e ina muradi.

Cikin zafin nama tare da sihiri ta bi iska ta iso gaban su da sauri ta finciko Yasiraht tare da shiga tsakaninsu tana wani irin kalo ma d'auke da alamomin tambaya Samar da har zai yi magana ko me ya tuna sai ya nuna kujeransa da yatsa nan tabi iska ta iso gabansa tayi kasa-kasa tukun cikin isa da mulki ya taka kan matakalar ya zauna a kan kujeran tukun ta tashi da shi sama ta tsaya a sararin samaniya.

Hajiya Nafisatu ganin dare yayi gashi Uwani zata kawo mata ruwan zafi da sauri taje kitchen (madafi) taga ko ruwan bata d'aura ba ga kuma abincinta bata ci ba, gass ta kunna ta d'aura ruwa sai da yayi zafi ta juye ta d'auko zata tafi wata zuciya ta ce"anya Uwani yau lafiya tunda muke da ita bata tab'a mana haka ba barin kai ruwan nan inzo in duba ta.

'Dakin Uwani ta nufa nan ta sameta a k'asa dai-dai k'ofar fita a kwance a k'asa idonunta a sama duk sun kafe, ganin haka ba k'aramin razana tayi ba ta kira sunanta Uwani! Uwani!! Uwani!!! Ido ta zaro tare da d'aga hannuta ta ga ya saki da sauri ta juya tayi d'akin Abba da gudu ta shiga tana fad'in "Alhaji Uwani! uwani!!". Sam bata cikin hayyacinta sai da ya rik'ota ya soma mata addu'a ya ce"lafiya me ya samu Uwanin?.

Hannuta ya kama suka nufi d'akin yana zuwa ya ganta nan ya d'aga hannuta ya ga ya saki nan Abba ya saki salati don ya gane Uwani ta rigamu gidan gaskiya hannu yasa ya rufe mata idanunta tare da d'auko zanin ya rufe ta ya gyara ta a gefe d'aya hannu Hajiya Nafisat ya kama yana bata kalamai masu dad'i da kwantar da hankali ya kai ta d'aki ya fita ya kira Yasar ya masa bayani tare sukaje aka kira Limamin unguwansu tare da wasu makwabta, a dare aka nimi dangin Uwani aka suturta ta tayi kwanan keso.

Yasiraht sai da safe da ta tashi taga gidansu a cike nan ta tambayi hajiyarta me ke faruwa nan ta fad'a mata take taji wani zufa na keto mata ta razana sosai wato jiya ba mafarki takeyi ba asai da gaske abunda jiya ta gani a bacci ya faru nan ta fara hawaye duk wani tsoro tafaraji a haka aka fita da Uwani aka mata sallah aka kai ta gidanta na gaskiya Allahi Akbar rayuwa kenan.

Rash
Sanah
Ku biyo mu.

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts