New Post

Tuesday, 9 May 2017

'YAR MAFIYA.. 5

�� *YAR MAFIYA.....*��

*Rash Kardam*
        *Sanah S Matazu*
*N. W. A*
Page
*5*

Makaranta Mata da ke garin Kano ta dabo tumbin giwa aka kai ta S Marafa da Yasar su sukaje tare da ita aka gama komai aka bata JSS1A su Abba da Yasar basu bar makarantar ba sai da suka tabbatar da an had'ata da Senior (Na sama da ita) kafin suka mata sallama tana hawaye Yasar na hawaye yana rik'e da hannunta da kyar Abba ya raba hannusu suka shiga mota suka bar makaranta.

Rayuwan Yasiraht haka ya cigaba da gudana aciki kwalejin mata da ke garin kano tana karatu dai-dai gwar-gwado sam bata faye yawan kawaye ba sai k'awarta d'aya wato Shukura Adam ita 'Yar cikin garin Kano ne nasu yazo d'aya komai tare sukeyi wasu har suna musu lak'ani da 2stars(taurari biyu) don itama Shukura ba baya bace gurin kyau amma ita bak'a ce.

Seniors da yawa suna kawo musu farmaki akan suna son su da School daughter(d'iyar makaranta) duk wacce ta tsare su sai suce mata a gida an hanasu yin School Mummy(uwar makaranta) wasu daga lokacin da sukak'i amincewa musu zasu fara gallaza musu da tsangwama.

Yau take Visiting day (ranar ziyara) duk wani d'alibin da ke makarantar yayi kitso tare da wanke uniform d'insa na makaranta kowa ya fito tsaf sabida zuwan iyaye da yayu/kanne, hakan yake a gun Yasiraht don gayu tayi tana jiran iyayenta can taji wata 'yar ajinsu tazo tana cewa wai ana kiran Yasiraht S Marafa a bakin gate(gareji) yihuhuhu!!! Tayi wani tsalle tare da rawa Shukura sai dariya ta ke mata ta ce"kai Yasiraht irin wanan murna haka?". Yasiraht ta juya ido ta ce"ya bazanyi murna ba yau My Yasar d'ina ya zo tare da Abba na da Ummi na ga swt Yasmin d'ina". Shukura tayi murmushi suka mik'e suka sanya kaya suka fita tare.

Ko da sukaje gunsu Abba da gudu taje gun fa rik'e hannusa tare da fad'i i miss you my Yaya na(nayi kewar ka ko rashin ka)Yasar sai dariya ake mata tukun tazo ta rusuna ta gaida su Abba kayan abinci suka kawomata tare da girki mai dad'i haka sukayita hira har lokacin tafiyansu yayi wanda da kyar sukarabu.

BAYAN SHEKARA UKU.......

Wata kyakwan Yarinya muka hango sanye cikin uniform d'in makaranta  ta fito sai zun b'ure baki takeyi, Yasar ne ya kalleta ya ce"My sisi dole yau ki koma makaranta tunda ke ki ka zab'a da kanki". Yayi maganar cikin tsokana tare da yi mata gwalo biyo shi tayi da gudu zata kwad'a masa jaka dake hannuta ya tsere, Abba ne ya fito wanda hakan yasa suka nutsu mota suka shiga suka d'au hanyar kano tun a mota take kumbura har suka iso makaranta ko sallamar kirki bata musu ba sabida fushin da takeyi, ta saka junior (na k'asa da ita) suka tayata d'iban kayan ta ta tafi hostel.

Sam yanzu bata jin dad'in makarantar sabida an cire Shukura a makarantar yanzu bata da k'awa sai wata Najwa da ke damunta akan suyi kawance dole ba yanda ta iya ta fara bin Najwa sabida Najwa ta faye naci, wani saran da Yasiraht ta samu sam yanzu bata yawan addu'a komai yin shi take batare da ta nimi kariya daga gun Allah ba.

Wata rana ta kwanta cikin mafarkinta ta ganta a cikin dokar daji sai jin tayi ana kiran suna ta kuma muryan bibbiyu yake fita ga daji ba haske ko tafin hannuta bata gani sai daga can nesa ta hangi wani haske cikin sauri ta k'arasa nan taga wasu irin halita tare da jajayen kaya ajikinsu suna cewa" Yasirah mu na gayyatar ki cikin mu ki zo zamu baki matsayi babba". Muryan mutane dayawa takeji take ta toshe kunnenta aiko sai guri ya fara tsawa rugugugu!!! Tamkar zai zaga kasa ta shiga ciki ko ina na jikinta b'ari yakeyi.

Kasan gurin ne ya fara darewa gida biyu nan tasoma ja da baya tana gudu yana tsagewa ko da ta kalli cikin k'asan da ya tsage ba komai ciki face kogon jini da kwarangwal suna kiranta. Cikin ihu da k'araji ta farka sai gumi takeyi sam ko addu'a ta kasa bare tasamu nutsuwa Sanah ta ce"ni ko anya Yasiraht tana addu'a?". Can na tsaya tunani na ce" ni dai ganina da ita na k'arshe da tayi addu'a tun tana JSS2 aji biyu a zango karatu na farko(first term) Sanah ta jin-jina kai(lalle tana sakaci da addu'a kamar yanda wasu acikin mu suke wasa da addu'a ma kansu bare 'Ya'yansu dan Allah mu kula muringa addu'a don neman kariya Allah ya kare mu da iyalan mu ameen).

Ku biyo mu.
Rash
Sanah

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts