New Post

Tuesday, 9 May 2017

'YAR MAFIYA..18

�� *'YAR MAFIYA....*��

*Rash Kardam*
        *Sanah S Matazu*
*N. W. A*
Page
*18*
Yasar yayo kansu cikin rud'ewa ya d'aga Yasmin ganin yanda jini ke zuba wasu mutane ne suka taimaka masa suka d'aukesu sukai mota cikin rudu ya shiga ya ja motar suka nufi T.H ko da sukaje emergency aka shiga da su likitoci sun dad'e akansu kafin babban su ya fito fiskansa ba alamar murmushi, Yasar ya taso da sauri yazo gun Likitan ya ce"Likita ya jikin su jinin da ke zuban ya tsaya?". Cikin sanyin jiki Likita ya dafa Yasar ya ce"Babban ta farfad'o yanzu haka". Yasar ya ce"Alhamdulilah!". Likita ya sake duban Yasar ya ce"kai musulmi ne kuma ko da yaushe ana so musulmi ya kasance mai hakuri da juriya da amsan kaddaransa, sannan Ubangiji yana mana kyauta wanda zamu saba mu shaku da kyautarsa rana d'aya shi da yafi muson abunsa sai ya d'auke".

Likita ya nisa ya cigaba da ce wa"inason kayi hakuri Allah yayi rasuwa ma k'araman...". Take bakin Yasar yasoma b'ari ji yayi duk wani hanyan tafiyan jininsa ya tsaya da aiki kujeran da ke gefen sa ya zauna tare da furta"Innalilahi wa inna ilaihi raji'un ya Allah ka jik'an Yasmin". Sai da ya d'au mintuna likita na kwantar masa da hankali kafin ya ciro waya ya sanar da su Abba suna Asibiti yazo yanzu.

Jikin Yasar a sanyaye ya ce"Doctor zan iya shiga na gansu?". Doctor ya ce"eh ba matsala zaka iya shiga". Da kyar Yasar ya iya d'aga k'afarsa ya shiga d'akin gun Yasmin ya nufa ya sanya kunnesa a k'irjinta yaji ba alamar numfashi ya d'aga hannuta ma haka ya saki jikinsa a sanyaye yana furta"Innalilahi wa inna ilaihi raji'un". Ya juya gadon da Yasiraht ke kwance nan ya ga idonta  a rufe amma tana wasu surutu a hankali wanda sai ka kai kunneka kusa da bakinta ka iya jin mai take fad'a.

Da sauri ya isa gadon ya sunkuya dai-dai bakinta ya ji tana fad'i " bazan tab'a yarda ba ku bada jinin Yasmin d'ina, Najwa kece jagoran d'auko ta har ki yanka ta da hannu ki to tabbas sai na d'au fansa da ga yau ba mutunci a cikin k'ungiya yanda kuka bada jinin Yasmin ma dodon tsafi duk wanda yake da hannu a cikin abun sai yayi na dama sai na fitini kowa a k'ungiyan nan wannan alk'awari na d'auka ma.

Abba ne suka shigo Hajiya Nafisatu sai kuka takeyi a asai likita ya musu bayani a waje suna shigowa Yasar ya d'ago da sauri ganin su Abba ne ya niyyan fad'a musu Yasiraht ce tayi sanadin mutuwar Yasmin take bakinsa ya rik'e ya kasa furta komai sai b'arin da bakin ke yi.

Ku biyo mu

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts