New Post

Friday, 26 May 2017

YAR MAFIYA 20

�� *'YAR MAFIYA....*��

*Rash Kardam*
        *Sanah S Matazu*
*N. W. A*
Page
*20*

Cikin salon tsafi da sihiri Yasiraht tayi gir-giza ta dawo wani irin hallita kamar kada ta tayi kan Shany gadan-gadan, Shany ta ciro sanda tsafinta ta nuna kadar amma ina sai sandan da ya narke ya koma ruwan wuta ya zube a k'asa Yasiraht ta fashe da wani matsanacin dariya bakin ta yana fitar da aman wuta sai hayaki yake yi ta ce“kee Shany ai kun makara don yanzu sai kun raina kan ku sai kunyi nadaman jawoni cikin ku do  zan zame muku k'adangare bakin tulu hahahaha!!!…".

Ta kece da dariya sai da tayi mai isarta ta tun k'aro Shany tana fesa wuta a bakinta Shany ta soma ja da baya Yasirah ta yi wasu surkule ta ke wajan yasoma juyawa Shany tasoma ihu, Yasiraht ta na isowa ta fara fesa mata wuta Shany na ihu sai da ta bata wahala tukun ta kece da dariya ta ce“Shany ba zan kashe ki yanzu ba sai na baki d'an lokaci ki kuma kai ma Najwa labari in har ta kuskura tashiga gonata to sai wata ba ita ba".

Yasiraht na gama fad'an haka ta b'ace bat Shany jiki ba kwari ga shi duk taji ciwo zobenta ta murza take itama ta b'ace sai a gidansu Najwa ta bayyana.

Najwa duk tayi kuka har ta gode ma Allah masu aikin gidan ta kira ta shaida musu mutuwar kakanta a dare aka gyarata aka mata wanka washe gari da safe aka mata sallaha aka kai ta makwancinta Najwa duk ta dawo wani iri ta na tunanin kalan fansan da zata d'auka Shany ta bayyana a hankali ta taka har zuwa kusa da Najwa ta dafata nan ta soma bata hak'uri ta kuma shai da mata abunda ya faru wani gwauro numfashi ta sauk'e a fili Najwa ta furta “tabbas Yasirah ta mana nisa amma ko ta halin k'ak'a sai na rama sai na d'au fansa. A haka akayi kwana bakwai tukun Najwa suka soma shirin komawa makaranta.

Yasirah tana b'acewa bata bayya na ko ina ba sai cikin dajin makarantansu tana dariya nasara wai ita ke da wannan zobe da matsafa da dama duke nimansa sai da ta sai ta kanta tukun ta koma cikin hostel.

Najwa ko da ta dawo tana bibiyan Yasirah amma a b'oye don yanzu Yasirah tsoro take bata ko a gun mitin Samar yanzu yana d'an shakkar Yasirah don yanda take da zoben hannuta.

A haka su Yasirah da Najwa suka fara jarabawansu ta gama makarantar gaba da primary yanzu Yasirah ta samu 'yanci gashi duk ranan mitin sai ta kawo musu tun d'aya ko biyu an shayar da jininsa.

Ku biyo mu.

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts