BABBAN KUSKEREN
DANA TAFKA
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-46~50.
Da sauri yayi kanta, ganin haka, tasoma ja da baya, jikinta sai bari yakeyi. Haiydar yana zuwa kutu ball yayi da boket d'in. Yana huci tamkar wani namijin zaki, yana jin yuwa yafito farauta. Indo ko ta mak'ure a jikin gini, sai b'ari take, don tunda take a rayuwanta, bata tab'a ganin fushi irin na Haiydar ba. Don in ta kali fuskansa, sai taga kamar na zakine yazo gabanta yana huci. Kanta ya nufo yana cewa"waya kawo ki gida na?.
"Meye had'in ki da wanke bedsheet d'in da na kwanta da matata.
Indo ko gani tsanani fushi ya had'u da tsoro, bata san lokacin da ta sulale, kasa sumamiya ba.
Haiydar ganin idonta sun kafe, hakan ya tabbatar masa da suma tayi, wuceta yayi ya nufi cikin gida, da fushinsa.
Falmi ko tana zaune a kan gado, takecin indimiee, wani gululun bak'in ciki ya k'ara tokaraansa, wannan wani irin iskanci ne?. A kan gado take cin abinci. "Mtsss yayi tsaki".
Cikin muryan shagwab'a tace"My Haiydar ka dawo?.
"Bayan tafiyanka yunwa ta dame ni da...
"Keee wa ya kawo min wannan bak'ar mai ido kamar na mage, gida na kuma don iskaci da rainin hankali, zanin dana kwanta da ke take wankewa.
"Mtss shikenan nikam nagama yawo, yarinyanan zata rainani.
"Ta gama sanin sirina.
"Shikenan nikam kin gama dani mtsssss.
Falmi tace"to ya kakeso nayi, ni kasan ko a gida ita, take min wanki. Hatta under wears d'ina ita take wankewa.
"Mtsss sai kiyi tayi ae.
Falo ya fito tare da bata guri, ganin zaman gun bazai masa ba, ya nufi d'akinsa cike da kunan zuciya.
Falmiko tana gama cin abinci a gun ta bar kwanon, ta sake kwanciyarta.
Indo ko ta dad'e a sume a gun, sai da ruwan da ya zuba ya iso jikinta, hakan yata daman farkawa. Hasken ranane ya haska mata ido, da sauri ta mik'e, cike da tsoro, tace"yanzu ta koma gidane ko ta shiga gidan?.
Wata zuciya tace"in kika tafi baki gama aiki ba, wani tashin hankaline. A hankali tashiga gidan d'akin da Falmi take ta nufa, poss d'inta ta d'auka, tafito falo da shirin ko ta kwana.
Haiydar ne ya fito, nan rake ta soma b'ari. Cikin fushi da muryan hargowa yace"ke mai kikeyi a cikin gidan nan da baki tafi ba?.
Kasa bashi amsa tayi masifa ya cigaba dayi, wanda hakan ya tashi Falmi ta fito. Haiydar janyo Indo yayi yace"ki fita min a gida kar na k'ara ganin k'afarki a gidan nan sai na karya ki.
Falmi tace"miye haka wacce zata min aiki zaka kora?.
"Kasan dai ni ban iya aiki ba ko?.
"Ita zata na mana girki da sairan aiki.
Haiydar ya kulu iya kuluwa, yace"kee miye aikin ki da baza kina aiki ba?.
"Ni fa ka ganni ko agida ruwan Lipton sai an dafa min.
Cike da ta kaici yace"baki isa ba to ni bana son girkin yar aiki. Ya wuceta fuuuu yayai d'akinsa qofar ya bako ya kwanta yana mai takaicin abunda ya faru, "daman haka halin Falmi yake?.
Falmi tana zuwa d'aki Mum d'inta takira, sai da ta sanar mata da komai.
Mum tace"yayi kad'an daga zuwanki zai fara fida halinsa to bai isaba wallahi.
"Yar'aiki kuma kamar ta zauna daram, dole Indo ta dawo cikin satin da zamu shiga, tunda baki saba aiki da kanki ba.
"Ki bar min komai a hannuna dole yayi biyayya.
Falmi cike da jin dad'i ta mata sallama, ta kashe wayar.
DEDICATED TO
AISHA MUHAMMAD
(MAMAN ABDUL SHAKUR)
RASH LUV✍
[5/28/2016] Rash Karda
BABBAN KUSKEREN
DANA TAFKA
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-51~55.
Indo tana fita, kuka take maras sauti, tana rokon Allah ya fitarta ya bayyana mata da danginta. Haka har ta iso gida, tana zuwa bata huta ba ta kama wasu ayyukam, da zatayi ma Hajiya, gashi sun k'aru sabida yan biki.
Falmi kuwa bata sake leko falo ba sai dare, da yunwa ya dameta, wasu matsatsun kaya tasaka. Haiydar na falo yana kalon tashar BBC WORLD ta shigo sai karairaya rakeyi, kalo d'aya ya mata ya kasa d'auke kansa, kasancewan bai da hak'uri. Take ma manta fushin da yakeyi da ita, ganin taki zuwa kusa dashi, tashi yayi a hankali yaje ya rikota, cikin rad'a yace"haba baby na fushin ne har yanzu?.
Sai da ta d'anyi farrr kafin tace"ni yunwa nakeji fa.
Hannu ta ya kamo sukaje dinning, asai yamusu take away. Nan yaringa bata a baki tana ci sai da ta k'oshi, ya sun kuceta sai d'akinsa, nan labarin ya canza.
Hajiya Fiddausi, sai datayi shige da fice, tasamo kan Haiydar, ya yarda Indo ta dawo gidan da zama tana musu aiki. Hajiya tace"ma Falmi ta bari sucika wara sai Indo tazo, a kwai abunda takeyi ne. Falmi badan taso ba ta amsa ma Mum d'inta.
Kwanaki sun tafi yau 3weeks da bikin Falmi, tasoma caza ma Haiydar kai, Haiydar duk lokacin da yazo da buk'atarsa Falmi tayi burus dashi, ko kuma in tabashi had'in kai sau d'aya, to ba zai k'ara ba. Haiydar har ya d'an rame.
Mum takira Falmi tace"to ba zama zakiyi ki zuba masa ido ba.
"Zaki fara tatsansa ne mu had'a jari.
Falmi tace"Mum to taya zan tatse sa da yawa bacin akwai komai a gida?.
"Mtss kee sai kace ba mace ba, bakisan tanda zakiyi ki samu kud'iba.
"Kina tambayansa mana.
"Ko kuma in yazo kwaciyan aure dake, kice sai yazuba kud'i ke bazaki iya ba.
Falmi tace"to Mumcyna hakan zanyi ma kawai.
Mum tace"yauwa yar albarka. (Kira gareku mata masu irin wannan galin, idan mazajenku sun zo muku da buk'ata, kuce sai sun baku kud'i, wannan BABBAN KUSKURE NE, aikata hakan haramci ne dan Allah akiyaye).
Da yamma Falmi tayi wanka tayi kyau sosai, kasancewan bata girki Haiydar ke sayo musu tayi zaman jiransa.
Haiydar ko da sallamansa ya shigo gida, tunda ya kyalo Falmi, ya had'iye wani yawu. Take yaji jikinsa ya mutu, dining ya wuce ya ajiye abinci da ya sayo musu, Falmi ko bata iya cemasa sannu da dawowa ba. Sai shine yace"ya gida fatan kin na lafiya?.
Sai da ta d'au lokaci, kafin tace"lafiya lau nake. 'Dakinsa yaje ya watsa ruwa ya saka 3quater da singlet ya fito, a dining ya ganta. Shima can yaje ya zauna, ya kaleta yace"ki d'auko plate da spoon kiyi serving d'in mu. Sai da ta ya tsina fuska taje ta d'auko ta dawo, har ta zauna yace"ruwa fa ko sai mun gama ci za'a d'auko?.
"Mtssss ta yi tsaki ni na gaji da yawan tashi.
Sai da suka gama ci, Falmi ta zo jikinsa ta zauna, don yau tanason ta fara wankansa, tunda tagane shi mai yawan bukatane, wasani tafara masa, wanda yasaka hankalinsa tashi, gashi kwana biyu Falmi ta hanasa kanta.
Shima biye mata yayi suka dulmuya, sai da taji zai wuce ta mike zubur, cikin dashashiyar murya yace"Falmi karki ki amincewa dani.
"pls ki taimaken una cikin yanayin bukata.
Kafad'a ta ya tsina tace"ni bazan iya ba.
Cikin yanayi tausayi tafara"pls My Falmi ki taimaken dan Allah ina buk'atarki sosai.
"Duk abunda kike buk'ata zan miki matsawan zaki bani had'in kai.
Sai da tayi wani murmushin mugunta tace"kayi alkawari ina fad'i abunda nakeso zaka bani?
Da sauri ya amsa mata"da eh! Zan baki koma miy ne.
Falmi tace"kud'i nakeso masu yawa.
"Haiydar jikinsa na b'ari ya tashi ya duba Aljihun wandinsa ba wani kud'i masu yawa, sai 10k ne kawai don d'azu a gun aiki, yayi sadaka da kud'ade'en da ke jikinsa, ma masu bara, duka dubu goma ta d'ebo yace"ga abinda suka rage min nan.
Falmi tace"nawane wannan don naga da alama basa da yawa?.
Haiydar yace"10k ne kawai bana da kud'i a jikina suna banki.
"Mtss mai dubu goma zasu min, asai baka shirya jin dad'i ba.
Haiydar kamar zaiyi kuka yace"haba Falmi ki taimaka ma halin dana ke. Zugunawa yayi akan gwiwansa, don bayason abunda zai b'ata mata rai.
"Mtsss to mai kake so na maka ne?.
Da rauri yace"ki taimaka min.
Ummmm"zan iya barinka kayi kiss a 10k amma fa da sharad'in bazaka wuce haka ba?.
"Eh na yarda in har zaki bari namiki d'an kiss d'in.
Okay!. Da sauri Haiydar ya taso yazo zai rungumeta, Falmi ta ja da baya, tana masa kalon raini wayo.
DEDICATED TO
AISHA MUHAMMAD
(MAMAN ABDUL SHAKUR)
RASH LUV✍