New Post

Friday, 7 July 2017

Babban kuskure.. 31-45

����������������
����BABBAN KUSKEREN����
       ����DANA TAFKA ����
                 ������
                    ��������
                       
                       NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-31~35.

Firdausi ta kirata, suka taho tare, can gefe ta zauna, sai da ta gaidasu. Alhaji Hashim yace"baiwar Allah ya sunanki?.
Matar nan tabashi amsa da"sunana Safinatu".
Alhaji Hashim yace"matana tamin bayani yanda kika fad'a mata.
" ko zan iya sanin mai ya kawoki Bauchi?.
" nan take matar ta fara kuka, tace"Ni sunana Safinatu, ni haifafiyar garin Yola ce.
"Ina gaban k'anin mahaifina, na taso cikin kulawa, har na girma, duk ran laraba, ake cin kasuwar garin mu, kuma duk ranan laraba, na ke kai tallen nono, cikin garin mu na Girei, a haka har Allah, ya had'ani da Muhammadu, shikuma yana kawo shanu, duk ran kasuwa, yana da zama'a Rugan Ribad'o. Ko da muka dai-daita kamu, nan iyayena suka mana aure. mijin dana aura ya kasance yanada garken shanu sosai, hakan yasaka wasu ke jin haushinsa. Har suna masa gorin zuwa yayi, duk da shima bafulatanine, kwanaki suka tafi, kulum garken shanunsa sai hab'aka yakeyi, hakan yasa mak'iya suka fara kawo masa hari. Tundaga likacin ya fara sanar dani, duk da banjin dad'i, ina fama da laulayin ciki. Bayan wasu watani, lokacin cikina ya fito, dadadare muna kwance, wasu yan rugan mu suka zo donsu kashe, Muhammadu su kwashi dukiyarsa, ganin hakan ya d'ebi, kud'i yaban da wasu hotuna, tare da awarwaro, yace na rike wannan. Ya kad'a shanunsa muka d'au hanya muna tafiya, su Sale suka biyo mu, sunyi artabu da Muhammadu, da kyar Allah ya basu ikon kwad'a masa sanda'a kafad'a, ganin bazai iya kare kansaba, yace"Safinatu ki gudu ki tafi garin Gombe ki nimi yan'uwana, suna Gombe. Kafin yayi wani magana sun kwad'a masa sanda take jini yasoma zuba, a gun ya fad'i ko motsi bayayi. Ganin ina kuka Sale yace"ku kamata don zata iya tona mana asiri, jin haka nasa gudu.
Haka har Allah ya taimakeni na fito bakin titi, saiga mai mota na shiga ya kaini, cikin gari nasamu motar Gombe ta tashi, sai na Bauchi, nan wasu sukace, idan ina sauri na shiga na Bauchi, haka nashiga motar Bauchi, ko da na iso yan kud'i na sun k'are, hakan yasa nayita yawon bara, gashi bansan ta inda zan fara niman dangin Muhammadu ba.
Alhaji Hashim ya nisa, Yace"naji labarinki, kuma a yanzu niman mutum batare da wani Address ba, ba k'aramin tashin hankali bane. Awarwaro ba zai zama abun shaidan da har za'a gano suba. Firdausi tace"Alhaji mai zai hana tana mana aiki sai ana biyanta, tunda Lami tayi aure wancan Satin.
Alhaji yace"haka za'ayi.
Ya kali Safinatu yace"Safinatu sunanki ko?.
Tace"masa eh! hakane.
Yaci gaba da cewa"zaki iya yin mana aikatau, ana biyanki duk wata?.
"Kuma zamu baki d'akin da zaki zauna har sai lokacin da kika buk'aci tafiya?.
Cikin girmamawa tace"eh zan iya.
Alhaji yace"Alhamdulilah! Firdausi zata gwada miki komai.
"Sanna salary ki a wata dubu shabiyar.
"Tace"nagode Allah ya ban ikon kiyaye komai.
Haka tamik'e ta koma d'akin, tundaga wannan rana tadawo itace wankin kayan Fatima da wanke-wanke, ga shara, abunci sai da Firdausi ta koya mata. Duk wani abu ita takeyi. Ana haka  har ta haihu, cikin ikon Allah a gida bataje Asibiti ba. Ranan suna yarunya taci Sunan Aisha, amma tana kiranta da Indo, haka rayuwansu ta kasance.

               DEDICATED TO
            AISHA MUHAMAD
   (MAMAN ABDUL SHAKUR)
     
             ��RAS LUV✍��
5/27/2016] Rash Kardam ����������������
����BABBAN KUSKEREN����
       ����DANA TAFKA ����
                 ������
                    ��������
                       
                       NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-36~40.

Aishatu Indo ta girma sosai,, gata da wayo, Indo tana d'ibi dani amma wasu abubuwanta na haifinta ne, hatta muryanta irin nasane, kwayar idonta, yatsun k'afarta duk nasane, bak'in fata na ta d'auko. Gata da gashi kamar me, ganin Indo tayi wayo ga Fatima tana zuwa makaranta, ko d'an abu ya had'asu, karara Fatima ke mata gori, Aisha tayita kuka. Hakan yasa na duba wani private school d'in da ke nesa da gidan mu nasata, 30k ne kud'in makarantan, amma duk term zan bada 10k hakan yasa na sakata a Sky criest, kulum da sassafe zan shiryata, na d'aukota a kafad'ana da kafa zan kaita. Ina dawo gida nayi aikina da wuri inje na d'aukota. Da kud'in aikina nake biya mata, dubu shabiyar, duk wata ake bani kud'in aiki. Kuma ba abinda nake da kud'in kasancewan su suke ciyar damu. Sai in Sallah yazo nayi mana kayan Sallah.
Ahaka har Aisha tashiga Junior school, ina biyan mata, na sata a Islamiya, sam Aisha bata isa tayi k'awance da kowa ba Fatima wanda a tana Senior Secondary school, ta sata a gaba, yanzu Aisha itama tana tayani aiki, sosai mukeyi tare. Fatima tana SSS3, a Doll pine Maria, ta canza sunanta daga Fatima ta dawo Falmi, hatta Baban da Falmi yake kiranta, tana harka da kwaye wayayu, masu nutsuwan kenan Meesha da Xahra BB. Sune masu hankali. A haka ta kamala secondary school d'inta. Ko da result yafito sam baiyi kyau ba. Hakan yasa ta fara diploma, tana karanta estet management. Tana final semester, ranan ta fito a motarta, dai-dai Bauchi club, motarta ta tsaya. Ga dare ya farayi, tun daga nesa ta hango wani mota Range Rover baka, bakowa bane aciki face Aliyu Haiydar. Da kamar zai wuce ganin macece tana buk'atar taimako hakan yasa ya, ko da yazo da sallamansa ya mata, ta amsa. Yace"lafiya mai ya samu motarkin?.
"Wlh ina tafiya naji k'aranta ya canza, kafin nayi wata-wata ta tsaya. Bud'e motar yayi, yayi nasa iyawar taki tashi, hakan yasa yace"in bazaki damuba in taimaka miki.
Tace"ba matsala. Wayarsa ya kira mai masa gyara yazo ya d'au motarta, tare ma da bata address d'insa, abunda yasa bata damu ba, taga Haiydar cikin kayan Police, shiyasa tasan ba zai cutarta ba.
Motar suka shiga ya kaita har qofar gidansu, zata fita tace"nagode da taimako gashi zamu rabu bamu san juna ba.
Murmushi yay8 yace"Sunana Aliyu Khaleeb Baba, ama ana kirana da Haiydar wasu kuma sukan ce min AK Baba. Cikin yanga tace"wooow nice name!".
"Ni kuma sunana Fatima Hashim Marad'i, amma ana kirana da Falmi.
Cikin fara'a yace"suna mai dadi.
"Ku ya  Niger ne?.
Tace"masa eh zamane ya kawo mu Bauchi.
Nan sukayi exchange d'in phone number, tamasa godiya tashiga gida.
Kwanki sun tafi, yanzu Aisha tana Jss3 suna third term,  ranan jumma'a ranar da Aisha bazata manta ba a rayuwanta, shine randa ta wayi gari mahaifiyarta ta rasu, ranan tayi kuka, ta dawo bata kowa bata da gata sai Allah. Bayan kwana bakwai Hajiya Firdausi tace"yanzu sai ki maye gurbi Uwarki da aikin da kike ko kuma kisan inda dare ya miki.

                 DEDICATED TO
           AISHA MUHAMMAD
      (MAMAN ABDUL SHAKUR)

             ��RASH LUV✍��
[5/27/2016] Rash Kardam ����������������
����BABBAN KUSKEREN����
       ����DANA TAFKA ����
                 ������
                    ��������
                       
                       NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-41~45.

Aisha Indo ba yanda ta iya, haka taci gaba da aiki a gidan, Hajiya da kanta ta rage mata Salary zuwa 7k, hakan yasa bazata iya d'aukan nauyin, karatunta ba ta hak'ura.
Aliyi Khaleed Baba, tun randa yaga Falmi ya rasa nutsuwarsa, kasancewan ya ganta irin matar da yakeso, gata fara sol, don shi tsarinsa bai son bak'ar mace. Masu karatu zamuso sanin,
  WAYE ALIYU KHALEED BABA(AK BABA).
Alhaji Khaleed Baba asalin d'an Bauchi ne shi, cikin k'aramar hukuman Sakuwa, dake garin Misau. Yata so cikin garun Bauchi yana aiki a kar-kashin Treasuring a yawon aikisa yaje garin Gombe suka had'u da Hajiya Khairat wanda take da zama a garin Gombe.
A haka akayi auresu da Alhaji Khaleed ya d'aukota suka dawo cikin garin Bauchi,
Suna da zama a State Low cost, bayan aurensu Allah ya azurta su da d'a Aliyu, sai da Aliyi ya girma sosai kusan shekara 12 kafin aka Haifi k'anwarsa Hasna. Wanda yanzu itace auta. Wanan kenan bari mu dawo labari.
Haiydar yakasa hak'uri takanas yazo gidan su Falmi, tun daga ranar suka sasanta kansu. Soyayya mai k'arfi tashiga tsakaninsu. Kusan kulum suna tare da juna, wata rana yazo gun Falmi tun daga nesa yaga, Aisha zata shiga gidan sam bata lura dashiba, horn ya mata sosai don tayi nisa cikin tunani. Sai da ya taka burki ya fito ya fara zazaga mata masifa. Ko da Falmi tadawo ta ga sai huci yakeyi, tace"My Haiydar mai ya faru haka?.
Nan ya fad'a mata laifin da yarinya tamasa.
"Mtsss miye na d'aga hankalunka, akan wannan yar shegen, da ba'a san ubanta ba.
"Uwarta tazo tayar mana ita.
Nan taba ma Haiydar kabarin komai harda k'arya aciki. Madadin Haiydar ya tausaya mata sai yaji haushinta.
Kwanaki sun tafi, magabatan Haiydar sun zo ansaka ranar Aure wata d'aya, sai shiri sukeyi, Falmi tasha gyara sosai, Falmi kasancewar yar casu ne, event tashirya bana wasa ba, tun daga rantalata suka fara event, har Friday idan nace zan tsaya baku labari, events d'in bikin nan da yanda komai ya kasance, charged d'in wayata zai d'auke, ban gama shiba. Ranar Friday aka d'aura aure. Duk wani abun al'ada anyishi, ranar yini da daddare abokai suka raka ango, sai da sukayi yan barkwanci, kafin suka musu sallama suka tafi. Haiydar ya rakasu ya dawo, Falmi tana ganin ya dawo, tazo cikin shagwab'a tafad'a jikinsa, azuciyar Haiydar kuwa cewa yake"wanna wata irin Amarya ce ba kunya, amma sai ya share wata zuciya tace"Son da take maka ne yasaka haka.
Falmi bata bari sukayi Sallah farinci da godiya ma Allah ba, ta fara aikin sha-shafa Haiydar tare da masa wasu salo, Haiydar kasa jurewa yayi ya d'auketa sai kan bed. Salon da ya mata, ya rikitata ranar Falmi taji jiki, kasancewa ta kawo budurcinta, Haiydar irin Mazan nane wanda zamu iya cewa shi Hariji ne, a ranan sai da ya gurjeta sau uku.
Da safe sai da yayi wanka yayi Sallah kafin, yazo ya mata wanka ya gama shiryata kena, wayarsa tayi k'ara ya d'aga, ganin daga office ne, ya kara a kunnesa tare da fad'in "Hello" daga d'aya b'an gare akace"Sir kazo Commissioner ne yazo yana son ganika yanzu, akan wani case d'in da'aka kawo.
Ba yanda ya iya dole ya fita, Falmi ko tunda taga 8:00 bai dawi ba, ga bedsheet d'in da suka kwanta ya b'aci, ko yaye wa batayi ba. Waya ta d'auko ta kira, Mum bayan sun gaisa tace"Mum ki turo min da Indo zata min aiki.
Mum tace"ke kina da glhankali kuwa?. "Kice na turo miki Indo gidanki.
Falmi tace"Mum Haiydar bayanan ankirashi a gentle a gun aiki, gashi bana iya tashi ne fa, kuma ban karya ba.
Mum tana jin haka ta gane sunyi abun garin, sai da tayi murmushi tace" gata zuwa yanzu.
Mum ta bama Indo kud'in mashine ta hau tazo. Sai da ta mata girki ta jera mata, Falmi tace"kee jeki d'akina ki yayi bed sheet d'in ki wanke. (Mata kira gareku, ku kasance masu kiyaye duk wani abun da ya shafi Sirrin Auratayyan ku, bakomai ake fad'a ba ko anuna, wanna Sirri ne tsakaninku).
Indo tunda ta gani, sai taji ba dad'i, amma ba yanda ta iya dole sai ta wanke. Ta d'ebo ruwa kenan ta fara wanki, sai ga Haiydar yashigo, tunda ya hango ta, yaji ransa ya b'aci. Ko da ya ajiye mota ya fito, dole sai yabi gefenta ya shiga gidan kasancewar qofar main falo yana rufe, yana isowa kusa da ita, karaf idonsa ya sauka kan bedsheet cikin kuna rai da zafin zuciya gami da wani kara yayi kamta da gudu.
Ni ko Rash ina ganin haka na tattaro yan komatsena, nasa ka gudu dan kar Haiydar ya had'a dani.

             DEDICATED TO
         AISHA MUHAMMAD
   ( MAMAN ABDUL SHAKUR)

              ��RASH LUV✍��

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts