YAR MAFIYA
Last Page.
Sanah S Matazu
Rash Kardam.
Kwanci tashi Yasiraht da Yasar zamansu masha Allah. Sossai suke kula tare da tarairayar junansu tsaye suke wajan addu'a basa wasa.Yasiraht kuwa ta lazumci nafiloli tare da azumin littinin da alhamis bata sake.
BAYAN SHEKARA GOMA.
Da gudu matashiyar yarinyar ta shigo da takardu a hannunta yar kimanin shekaru tara.
"Yee Mom and (Dad whare are you) kuna ina?"
Ta fada cinyar wata hakimar mace,mai cikar haiba da nutsuwa tana duba wani littafi mai taken Ta'alimul muta'alimi.
Ta shagwabe fuska.
"Kuna ji na kukai mun shiru?".
"Zonan Little Yasmin din Daddynta waya taba ki me kika samu kike murna".
Hajiya Yasirahr ta saki murmushi"kudai kuka sani walahi kaita batamun yarinya da salon shagwabarka".
"Daddy ka ji ta ko?".
"Ke kyaleta itama haka tayi bani labari insha cwt baby na".
"Daddy naci borading school".
Maganar tazo musu tamkar saukar aradu'cikin hargagi ta mike''ba'a gidan nan ba" jikinsa ya yi sanyi Yasiraht ta fashe da kuka''Daddy wai me yasa bata son bording sch ne kullum in nace ina so saita gwale ni?".
"Yi shiru little Yasiraht zata barki maza je ki dakinki ki huta".
Saida ya lallasheta ta yi shiru, sannan ya nufi dakin Yasiraht yana shiga ya sameta tana kuka idonta ya yi jajjir.
Kwantar da kai ya yi a kan kafadarta, ta juyo a hargitse"kana son farin cikin yarka ko? Baka tunanin kuncin da muka fada a baya ko?".
Birkito da ita yayi suka fuskanci juna"kiyarda dani Yasiraht walahi banda nufin kuntatta miki.Babu bawan da ya isa gujewa kaddararsa ita rayuwa mallakar kaddara ce kiyi mata kyakkyawan zato kowa fa da irin kaddararsa a rayuwa".
Ta yi shiru tana jinjina kalamansa, "shikenan na amince amma ta bari sai tayi jss three ta kara wayau da hankali".
"Yauwa Madam".
Sukai dariya gaba daya dai-dai lokacin ta shigo da gudunta,tana murmushi.Hannunta dauke da wani littafi mai kyau da daukar hankali idonta ya ciko da kwalla.
"Mommy a yau na karanta abinda yasa kike kina da makarantar kwana, tabbas Mommy hujojinki ababban dubawa ne kunga rayuwa keda Daddy walahi Mommy na hakura da makarantar kwana insha Allahu zanyi day gani ga ku ga su granny nafi son kwanciyar hankalinki".
Cikin murmushi ta bude mata hannuwanta da gudu ta karaso ta fada ta maida hannu ta rungumeta ta runtse ido hawayan farincikin ganin ta maida sunan Yasmin da kuma tuna rayuwarsu ta baya.
"Na tsani bording Yasmin SANADIN BORDING na zamo
YAR MAFIYA tai mun MUGUN DASHE acikin RAYUWATA".
Cikin kuka tace "Mom BAYAN WUYA sai dadi yau gashi da kika riki addu'a ta zamo KATANGAR KARFE a dukkan lamuranki.
NAYI ALKAWARI zan zamo farin ciki cikin rayuwarku Mom,da sanu zan muku BAZATA sai na tabbatar miki RUWA CIKIN COKALI ya isa mai hankali wanka".
Yasar yayi murmushi ya ce,"so please Madam we are free at last".
Ina labe na jawo hannun Rash muka leka bangon littafin ras! Gabanmu yadi a rubuce radau.
*"MAFIYA A SANADIN BORDING"*
Da gudu mukai baya muna murmushi.
Masha Allah Alhamdulillahi ala kuli halin yau gashi mun kammala wnnn kirkirarre takaitacan labari mai taken YAR MAFIYA.
_KU TSUMAYE A SABON NOVEL 'DIN MU MAI TAKEN SUNA *KISHIYAR TSAKAR GIDA.*_
JINJINA GA MASU BIBBIYAR BOOK DIN YAR MAFIYA.
Aunty Zain
Jamila Kaduna
Bilkisu Muhammad Kano.
Futhatulkuairi sidi be
Mermue
Aisha Muhammad (Maman Abdul shakur)
Kausar lurv
Aisha Mazoji
Meesha lurv
Munay
Khadija Candy
Anesah
Ummieluff
Rabee'atu
Jiddah Aliyu
Queen Miemi
Ummyn Aunty Asiya Malumfashi.
Nafisan Aunty Jamcy Kt.
Zee Mmn Khady
Saeed Bebeji
Teemah Cool.
Autar Hajiya
AshNur
Maijiddah Musa
Fulany Cerdiya
Mrs Zannah
Da duk masu bibiyarsa.Sadaukarwa kacokan gareku.
Bilkisu AmmaniChuchuna.
Ayshat A Sadeeq Chuchungaye hazika mataciyyar labaranmu wato me tacewa.
MUSHA KARATU YBK GROUP.
NAGARTA WRITER'SU
MATA MASU AJI.
Rash kardam hausa novels 1,2&3
Dandalin lubee mai tafsir
Duniyar littafin hausa
Ladies Novels World.
*TSOKACI*
Littafin yar mafiya kirkira ne dan fadakarwa kan masu sakaci da addu'a a koda yaushe bawa ya tunda tunawa addu'a KATANGA CE dake kare bawa daga dukkan fitunu da rudanin dny. A yau al ummah munyiwa addu'a rikon sakainar kashi wayoyi sunfi komai dauke mana hankali walahi muna sakaci muna cutar da kawunan mu addu a babban makami ce a garemu. ”
_Addu’a tana daga cikin qaddara, kuma sabab ce daga sabubba masu amfani, masu janyo alheri su yaye dukkan sharri. Haqiqa Allah ya yi umarni da addu’a a cinkin ayoyi masu yawa, ya ce,_
( ﻭَﻗَﺎﻝَ ﺭَﺑُّﻜُﻢُ ﺍﺩْﻋُﻮﻧِﻲ_ ﺃَﺳْﺘَﺠِﺐْ ﻟَﻜُﻢْ ﺇِﻥَّ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻳَﺴْﺘَﻜْﺒِﺮُﻭﻥَ
ﻋَﻦْ ﻋِﺒَﺎﺩَﺗِﻲ ﺳَﻴَﺪْﺧُﻠُﻮﻥَ ﺟَﻬَﻨَّﻢَ ﺩَﺍﺧِﺮِﻳﻦَ 60 ) [ ﻏﺎﻓر
_Addu’a ta qunshi buqaturuwar bawa da tsananin matsuwarsa zuwa ga Ubangijinsa, wadannan abubuwa ne haqiqanin ma’anar ibada.Ya ku bayin Allah! Haqiqa dimbin nassoshi na hadisan Annabi S A W sun zo game da falalar addu’a.Daga cikinsu akwai abin da Abu Dawud da Tirmizi suka ruwaito daga Nu’uman bn Bashir, Allah ya qara yarda a gare su daga Annabi_
_ya ce: “Addu’a ita ce ibada.” Tirmizi ya ce: hadisi ne kyakkyawa ingantacce.Kuma an karvo daga Abu Hurairah Allah ya qara yarda a gare shi ya ce daga Annabi)._
_ya ce: “Babu wani abu da yafi girma wajen Allah kamar addu’a.” Ahmad da Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibbana suka rawaito._
_An karbo daga Ubadah dan Samit (R.A) cewa, Manzo(S.A.W) ya ce, “Babu wani musulmi a ban qasa da zai roqi Allah da wata addu’a face ya ba shi ita, ko ya kade masa wani mummunan abu madadinta,matuqar ba ya roqi wani abin laifi ba ko yanke zumunci"._
_Sai wani mutum daga cikin mutanen ya ce: "Ashe za mu yawaita ke nan".Sai ya ce:“Allah Shi ne mafi yawaita wa.” Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta shi._
_Ya ku bayi Allah! Ku sani cewa ba a roqon kowa sai Allah, ba wani mala’ika makusanci ga Allah,ko wani Annabi mursali, ko wani waliyyi nagarta cce._
_Kuma duk wanda ya kirayi wani abin halitta ba Allah ba, Annabi ne ko mala’ika, ko waliyyi, ko aljan, ko kabari, ko makamancinsa, to haqiqa ya yi shirka da Allah Ta’ala, cikin ibadarsa, shirka da za ta fitar da shi daga musulunci._
_An karbo daga Ubadah dan Samit (R.A) cewa, Manzo(S.A.W) ya ce, “Babu wani musulmi a ban qasa da zai roqi Allah da wata addu’a face ya ba shi ita, ko ya kade masa wani mummunan abu madadinta,matuqar ba ya roqi wani abin laifi ba ko yanke zumunci"._
_Sai wani mutum daga cikin mutanen ya ce: "Ashe za mu yawaita ke nan".Sai ya ce:“Allah Shi ne mafi yawaita wa.” Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta shi._
_Ya ku bayi Allah! Ku sani cewa ba a roqon kowa sai Allah, ba wani mala’ika makusanci ga Allah,ko wani Annabi mursali, ko wani waliyyi nagarta cce._
*ALHAMDULILAH!! MASHAA ALLAH!! KUSKUREN DA MULAYI YA ALLAH KA YAFE MANA.*
MASOYA WANNAN LITTAFI DA BAMU SAMU DAMAN FADAN SUNAYENKU BA MUN GODE DA YAWA.
```KU KASANCE DA MU A LITTAFIN MU NA GABA MAI SUNA``` *KISHIN TSAKAR GIDA.*
BAN GAJI DA GODIYA BA.
Ayshat A Sadeeq Chuchungaye.
Husnah M Inuwa Ummu Samhat ubangiji ya bar zumunci mai dorewa.
*'YAR MAFIYA COMPLETE*
Ku duba
Sanahsmatazu.mywapblog.com
MUNA MUKU FATAN ALKAIRI
RASH
SANAH KU CE.
0 comments:
Post a Comment