New Post

Friday, 7 July 2017

Babban kuskuren 16-30

[26/5/2016]Rash Kardam ����������������
����BABBAN KUSKEREN����
       ����DANA TAFKA ����
                 ������
                    ��������
                       
                       NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-16~20.

Shewa sukayi, hiransu ta yaushe gamo sukeyi. Indo ko kitchen tashiga, ta d'aura girki, tukun tayi side d'in Falmi, sai da ta gyara ko ina, sannan ta je bedroom d'in Haiydar ta gyara, ta d'ebo kayansa da sukayi datti, ta wankesu, tana duba abinci. K'arfe uku da ta gama komai, ta jera a dining.
Falmi tace"ki kawo mana abincin mu falo".
Sai da da d'an rusuna tukun tace"to Aunty".
Taje ta zubu musu a cooler da plate takawo, Falmi cikin isa tace"kee wazai kawo miki ruwan ko ni zanje ba d'auko?.
Indo ta rusuna tace"ayi hak'uri zanje na sauke abune akan wuta.
"Mtss wuce ki d'auko kafin kiyi abunda zakiyi.
Indo ta jera musu komai agun gar zata tashi Falmi tace"ni zanyi serving d'in ko sai na fad'a miki?.
Indo ta tsuguna ta jera musu komai, tasaka ta mik'a musu, tukun ta mike ta nufi kitchen, don k'arasa sauran aikin da takeyi.
Sadeey tace"Falmi baki da k'yau, gaskiya kina juya yarinyan nan.
"Irin tsawan da kike mata ni har ta ban tausayi wallahi.
Meesha tace"niko yarinya k'yau ta min gata black beauty.
Falmi ta b'ata rai tace"mtss dad'ina da ke rashin ganewa, mai maza zasuyi da bak'ar mace.
"Bakijin yanzu cewa suke su Fara ko da mayya ce, suna sonta.
Xahrah tace"Falmi ae bazaki gane ba, sirrin k'yau yana tattare da bak'ar mace, don fara inda za'a kwashe farin ba komai zaki gani ba zai tsaban muni.
"Amma magaanan gaskiya Indo ta had'u ba k'arya.
"Sai dai rashin gyara da wayewa ne ya mata cikas.
"Ki kali tsarin jikinta mana, irin shape d'in da maza keso ne.
Take Falmi ta b'ata rai jin an kushe farare, don bak'aramin ji take da haskenta ba, gani take tafi kowace mace kyau.
A haka har suka cinye abinci su, Indo ta fito ta tattara kwanuka ta kai kitchen, tana ajiyewa ta k'oma d'aki, ko zama batayi ba taji k'aran shigowar motar Haiydar. Sai da gabanta ya fad'i, addu'a tafara yi, sabida duk lokacin da suka had'u, bata kwashewa ta dad'i.
Haiydar cikin takun isa ya shigo ckin gidan da Sallamansa, su Sadeey suka amsa, ganinsu yasa ya d'an saki fuska don yasan k'awayen Falmi ne sosai.
Gaisawa suka kafin ya wuce d'akinsa, yana shiga wani sassayan, k'amshi ya bugi hancinsa. Ajiyar zuciyzuciya ya sauke, kayansa ya cire ya nufi toilet, yayi wanka ya fito, k'ananan kaya yasaka, sabida ga bak'i, da na shan iska zai saka.
A hankali ya tako zuwa falo, Falmi tun da taga ya fito tasan in ba'a yi serving d'insa ba, zata sha surutu, cikin muryan isa ta fara kiran, Indo! Indo!
Indo dake d'aki jiki sai b'ari yake ta fito da sauri, ta rusuna a gaban Falmi.

                DEDICATED TO
                  AISHA MUH'D
    (MAMAN ABDUL SHAKUR)

             ��RASH LUV✍��
[5/26/2016] RashKardam ����������������
����BABBAN KUSKEREN����
       ����DANA TAFKA ����
                 ������
                    ��������
                       
                       NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-21~25.

                    Notice
   Masu karatu, na cire Sadiya a k'awar Falmi, zan maidata k'awar Indo, sabida wani dalili, ku kasance da YAR'GIDAN JARAWA.

Falmi tace"ke kwai bakinsan aikinki bane?.
"Bakiga Haiydar ya dawo bane?.
"Kije ki zuba masa abinci.
Indo ta mik'e jikinta ba k'wari, sai bari yake, ta nufi dinning area, Haiydar ko tun da ya hango ta, yayi yar karamar tsaki, cikin zuciyarsa ko cea yake"wato falmin bata ji, nace mata bana son aikina tana saka wannan wariyan taki ji.
"Dun taga ina qaunarta da yawa bana son abunda zai bata min rai.
Indo tana zuwa dining ta fara serving d'insa, sai da ta zuba maza jelop d'in shinkafa yaji Salad, sai k'amshi yake tash, gaskiya Indo ba ya bace gurin girki, don ta taso cikin horon aiki, shiyasa bata samun matsala game da iya girki, gyaran guri. Wani lokacin in tayi decoration ta gyara ka d'auka, ba ita bace tayi, wasu daban akayi hayansu sukayi.
Sai da ta zuba masa shinkafan ta tura masa gabansa, hannuta sai rawa yakeyi, a haka ta d'auko kofin glass ta zuba masa zob'o drink da tayi, ta d'auko zata ajiyea gabansa, hannuta sai b'ari yakeyi, bisa tsautsayi ya sub'uce ya fad'i aiko sai jikin, Haiydar, take rigansa tarine.
Nan ganjin cikin Indo suka soma shooky, hawaye ta fara yi.
Haiydar cikin b'acin rai yaga yanda ta b'ata masa jiki, ransa ya b'aci ya rasa mai zai mata, mikewa yayi har yazo zai tafi, sai ya fasa, d'auko juke d'in zobon yayi, ya shek'a mata a fuska. Ae ko sai cikin idonta take tafara mutsu-mutsu, tana niman hanyan saukowa, ganin abunda ya mata bai sheshi ba, sai da ya bari tana lalub'en hanya, ya saka k'afarsa ta fad'i timm! A k'asa, aiko ba shiri ta saki k'ara shiko ya mik'e abincin da bai ciba ya kima d'akinsa.
Duk abunda ya faru a idon su Falmi, cikin jin dad'i tace"kun gani ko ita kanta yariyan tsoronsa take, bare shi uban gayya da baya son ganinta.
Xahrah tace"to ki dai bi a hankali, don in wahala yayi wahala karta gudu.
Falmi tace"ina zata je wa take dashi a Bauchi.
"Ina ga ma la Uwarta cikinta tayi tazo ta haife ta.
"Don tun zuwanta sai tana cemana ubanta Indo na raye, kulum maganan d'ayq kenan.
Meesha tace"Xahra ya kamata mu wuce fa yamma tayi.
Falmi tace"kai Messha wato ke kike zugawa ku tafi ko?.
Duka sukace yau ai mun dad'e, mu zamu wuce sai gani na biyu.
Falmi tarako su har gate kafin ta koma ciki.
Haiydar ya fito zai wuce Falmi tace"darling bazaka ci abincin bane?.
Ko kalonta baiyi ba yace"nagode fita zanyi.
Ya na fita motarsa ya shiga bai zarce ko ina ba, sai k'aton katafaren gida, na alfarma, tun daga kan gate d'in, gidan abun kalo ne, horn yayi mai gadi ya bud'e masa, ya danna hancin motarsa, cikin gidan, gurin da'aka tanada don ajiye motoci, nan ya nufa, sai da ya ajiye motar ya fito. Gidan yana da girma sosai ko da na kali harabar gidan, zagaye yake da fulawas ja da yelo, sun matuk'ar k'awata gurin, a hankali yake takawa har yashiga cikin gidan, falo ya fara tararwa, ko da na kali falon, gaskiya ya tsaru komai na ciki Silver colour ne da baki, abun gwanin burgewa.
Daga nesa na hango wata yarinya wacce bazata gaza 17yrs ba, tana danna waya, farace sol kamar Haiydar, kuma suna d'an kama amma shi yafita kyau sosai, da sallama ya k'arasa shiga ciki, Hasna ta mik'e tace" Yaya Haiydar sannu da zuwa.
Cikin fara'a ya amsa mata, zama yayi a d'aya daga cikin kujerun dasuke falon.
Yace"Hasna kawo min abinci naci".
Cikin tausaya ma Yayanta, mik'e wa tayi ta nufi kitchen, abinci ta kawo masa, sai da tayi serving d'insa, tukun koma gefe ta zauna.

                DEDICATED TO
                 AISHA MUH'D
     ( MAMAN ABDUL SHAKUR)

              ��RASH LUV✍�� [5/26/2016]RashKardam ����������������
����BABBAN KUSKEREN����
       ����DANA TAFKA ����
                 ������
                    ��������
                       
                       NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-26~30.

Cikin zuciyarta ko tana tausaya ma yayanta, wanan wani irin aurene ace mutum sam bai isa da matarsa ba, ko yasata abu batayi, ga rashin kunya, ga kin jama'a, Hmm Allah ya kyauta.
Sai da ya gama cin abinci, Hasna ta kale Yayanta tace" Yaya Ya Indo?.
"Ina son yarinyan tana da hankali, ga kirki wallahi, Hajiya ma tana yawan tambayanta.
Wani harara ya sakar mata, wanda yasata jan bakinta tayi shiru, a zuciyarta ko cewa take"wai me Indo tayi ma Yaya ya tsaneta, ko sunata bai son a kira, kuma ni tafin Falminsa sau dubu wallahi.
"Mtss ina ma da itace matar yayan.
Maganan Haiydar ne ya dawo da ita daga duniyar tunani, da ta luka.
"Hasna ina Hajiya fa?
"Tana d'akinta.
Mik'ewa yayi ya haura sama.
Haiydar na fita Falmi ko kafad'a ta d'aga, alar ko in kula ta d'aki ta koma, WhatsApp ta hau taci gaba da chatting da friends d'inta.
        TUSHEN LABARI
Alhaji Hashim Marad'i, Haifafen d'an Niger ne, ya kasance mutum ne mai neman na kansa,  Allah yana bud'a masa, a haka har ya auri matansa Firdausi, bayan aurensu da kwanki ya tattara, yan dukiyarsa ya baro gari, ya dawo Bauchi da zama, shago ya bud'e, cikin ikon Allah, kasuwansa ta bun k'asa, Allah ya sanya ma dukiyar Albarka, nan da nan ya shahara ta ko ina a garin Bauchi.
Ana haka Matarsa ta samu cikin karkuso kuga kulawa da tattali, har cikinta ya kai wata tara, ana haka nakuda ya tashi, baiyi wata-wata ba sukaje Asibiti, nan aka karb'e su, sai d'akin haihuwa.
Bata dad'e sodai ba ta sankato, yarta fara sol, Nurse suka gyarata, suka dawo gida, ranan suna Yarinya taci sunan Fatima, Alhaji Hashim ya d'au son duniya ya d'aura ma fatima, baya son abunda zai tab'ata, Firdausi ma duk d'ayane, kula ta musamman suke bata, har yarinya tayi wayo ta girma sosai.
Fatima tana da shrkara biyar, tayi wayo ko ina tana zuwa har sun sata a makaranta.
Wani safiya ranar asabar, anyi ruwa sosai wata mata tana d'auke da k'aramin ciki, tazo qofar gidan Alhaji Hashim ta zauna, sai b'ari takeyi, ana haka Alhaji ya fito, ko da ya ganta, sai yaji ta bashi tausayi sosai. Mai gadi ya kira yace"kaje ka shigo da ita, gida ya koma ya samu Hajiya Firdausi, yace"ga wata mata tana buk'atar tai mako, ki bata duk abunda ya dace. Tukun ya fita.
Firdausi tasaka a ka shigo da matar sai yatdina take, ganin kayan jikinta yasa tace"ke biyo ni boys quater ta kaita, nan ta ce bara na kawo miki abinci.
Cikin gida takoma ta d'ebo abinci ta kawo mata, nan matan taci sosai, tayi godiya ma Allah. Ko da Firdausi ta dawo, tace" ina zaki kuma daga ina kike?.
"Matar tace"ni bakuwace banda kowa na fito garin Yola ne.
Firdausi tana wani isa tana yatsina tace"ok kya iya zama anan kafin mai gidan ya dawo.
Bata jira amsanta ba ta fita a d'akin, Alhaji Hashim bai dawo ba, sai yamma sai da yaci abinci, tukun yana hutawa, Firdausi tace"matar nan fa tana na.
"Oh! Na manta mai ta sanar dake gameda ita, don naga kamar ba'a cikin nutsuwarta take ba.
Firdausi ta mayar masa yanda matar ta fad'a mata.
Yace"kira min ita.

               DEDICATED TO
                AISHA MUH'D
   (MAMAN ABDUL SHAKUR)

              ��RASH LUV✍��

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts