New Post

Friday, 7 July 2017

Yar Mafiya 39-41

�� *'YAR MAFIYA*��

Sanah S Matazu
Rash Kardam
*39 to 41*

Kwanci tashi tsayin watanni ana neman Yasiraht amma babu ita labarinta.Jikin Yasar dai gashi nan yau fari gobe tsuma.
A haka aka samu numfashinsa ya dawo, saidai liitoci sun bada tabbaci zai iya rasa tunaninsa gaba daya.

Yasiraht na cigaba da samun kulawa wajan Sarauniya sossai, saidai  bata da karfin da zatai tafiya saboda jigatuwar da jikinta ya yi lokacin da Najwa taso hallakata.A hankalin ta soma takawa tana fita baki dajin tana kallon namun daji tare da taya Sarauniya farautar namun daji zuwa cikin dajin.

Kamar koda yaushe yauma tafe suke suna hira Yasiraht ta dubeta.
"Sarauniyya naji sauki ina son in koma gida saboda sanin halin da Yasar yake amma bakimun bayani wace ke ba".

"Cikin murmushi tace zakisan wacece ni bada jimawa ba,amma menene alakarki da wanda suke bibbiyar rayuwarki?".

Yasiraht ta sunkuyar da kai idonta ya ciko da hawaye tasa hannu ta share ta cigaba.

"Kawai tasowa nayi na tsinci kaina a cikin wannan harka amma kafin mutuwar Emeka ta bani labari cewa:

Asalin kungiyarmu ta mahaifin Samar ce,haifaffan garin Kano ne mahaifinsa Malam Sammani da me dakinsa Saudatu. Mahaifinsa mutum ne mai kwadayi da san tara dukiya tun yana saurayi harya girma iyayansa talakawa ne sossai suna zaune unguwar Yalwa a cikin Kano.Fahimtar hakan yasa suke yi masa nasiha sossai, amma baya ji idan yaga masu kudi baya tunanin tayaya suka samu dukiyar kawai burinsa Allah ya bani itaku ko kuma ya dinga biy-biyarsu yana su bashi aikin yi shima yayi kudin hakan yana batawa mahaifansa rai sossai.Lokacin da yai auran fari kwatsam yana matakin karatu s college kasancewar duk da rashin mahaifinsa ya tsaya masa matuka kan karatu suna level one ya soma samun matsala a jarrabawarsa hakan yasa ya shiga damuwa sabida ya dogara da karatunsa sossai  kwatsam ya samu kansa an masa tallar kungiyar kan cewar in dai ya shiga bashi ba faduwa a jarrabawa ga kuma kudi da zai dinga samu mudin zai bi dokoki bai jimaba ya amshi batun hannu biy-biyu lokacin bai yi auran fari ba sai da ya shiga aka soma jero masa dokokin kungiya babu fita in an shiga kuma duk wanda ya tona musu asiri kashe shi zasui.

Hajara itace diyar kanin mahaifinsa da ya mutu ya bashi a gidansu ta tashi itace yake matukar so, farkon shigarsa aka bashi kudi naira dubu dari biyar ganin kudin ya daga hankalinsa bai taba kama irinsu ba nan ya boye dubu dari uku ya nufi gida da dubu dari biyu nan ya zauna ya shiryawa mahaifansa karya kan cewar mahaifin abokinsane ya bashi aiki kafin ya gama makaranta suna yi masa aikin company wannan kudi an basu ne  dan farkon daukane duk wata za a dinga basu dubu hamsin mahaifansa sunji dadi sossai har gida suka taka gidan daya daga manyan kungiyarsu a zuwan mahaifin abokinsa ne tafi-tafi watanni naja ya soma shirin auran Hajara watansu biyar da aure ta samu juna biyu nan dodon tsafi ya nemi jininta shi kuma yace atabau bazai bayar ba nan suka nemi jinin mahaifansa mahaifinrsa ya fara badawa kawai sai wayar gari akai aka ganshi a mace.Bayan wata uku da mutuwarsa Hajara ta haifi kyakkyawan yaronta namiji yaci sunan kakansa ake kiransa Samar.

Kwanci tashi Samar na girma kyakkyawa dashi, sun shaku da mahaifiyarsa da kakarsa mahaifin Samar kullum cikin bibiyar shuganinsa yake harya gama sanin makamar aiki kaf kwatsam aka nemi jinin mahaifiyar Samar a lokacin yai musu tawaye da hadin bakin wasu cikin manyan abokansa kaf suka kakkashe manyan ya maye kujerar shugabanci wanda saida ya bada jinin mahaifiyarsa sannan ya hau a cewarsu dalilin da yasa suke bukatar jinin mahaifa saboda mutum bashi da wanda yafisu mudin  ya bada su to zai iya bayar da kowa tun Samar na shekara goma mahaifinsa yake koya masa zafi ya kware sossai sannan ya sashi makaranta ta hanyarsa suke samun shan jinin yara kanana tare da kswosu cikin kungiya. Samar na aji shida na firamari suka hadu da Najwa lokacin tana aji hudu shakuwarsu ta samo asaline daliin lesson na maths da yake musu  tsakanin gidajansu gida kusan goma ne ya rabasu. Shakuwarsu tayi tsanani sossai a haka ya gama primary ya faɗa secondary ita ƙkuma tana aji biyar yana jss two akai masa jumping ya tafi aji biyar yazana jarrabawa ya shiga aji shida lokacin ta tafi form one yana aji shida ta shiga form two tana aji uku ya gama secondary mahaifinsa ya nema masa gurbin karatu a Cairo.

Lokacin da zai tafi tasha kuka sossai.Asalin mahaifan Najwa haifafun garin Jos platue ne Hajiya Moma da Najwa ke kira da Moma itace ta haifi mahaifinta tare da mijinta wanda ya jima da rssuwa.Alhaji Shazali shida yayansa Shamsudeen Shamsu deen ya rasu ya bar Shazali hakan yasa Moma ta dauki so ta dorawa Shazali lokacin da ya kammala karatunsa yai aure ya auri abokiyar karatunsa Maryam mace mai nutsuwa da hankali shekararsu daya da aure aiki ya dawo dashi Kano yaso tahowa da Moma taki amincewa haka suka rabu suna kewar juna.

Zamansu a Kano zamane me daɗi da kwanciyar hankali shekararsu ɗaya suka haifi yara biyu kyawawa Najwa da yayanta Nura wanda suke kira Nur sun taso cikin so da kulawar iyaye uwa uba Kakarsu duk hutu wajanta suke yi cike da so da kulawa bayan Najwa da Nur akwai Fadil da Fadila daga su iyayansu basu sake haihuwa ba.

Lokacin da Samar yazo hutun farko sai mamaki ya ƙkamashi ganin yadda Najwa ta koma katuwa da ita yana ziyartar gidansu akai akai kowa ya sanshi wani zuwa da Samar ya yi gidansu Najwa suna hira take bashi labarin tana son bording schl ba ƙkaramin daɗi ya jiba amma bai nuna mata a ransa yana ayyana wannan lokacine ya dace ya jawo Najwa kungiya yadda zasu ji ɗaɗin samun mata matasa cikin tafiyar.Samar babu abinda ƴya fasa na zafi daya je karatu saima gaba saboda ya  damu waɗanda suka fishi gogewa kan harkar.Washegari ya zowa Najwa da tsafataciyar alawarsa ya bada babu jinkiri ta shanye a barta tun daga lokacin ta soma bibbiyar Samar sau da kafa kuma komai ya bukata babu jimawa take masa a haka yasa ta bashi jinin Fadil da Fadila kawai sai tsintar gawar yaran a kai a ruwan wankan su na boys quaters mutuwarsu ta girgiza kowa sossai bayan rasuwarsu aka kai Najwa makaranta nan ta soma jawowa kungiya member hakan yasa matsayinta ya girmama a cikinsu suna jss three ta bada jinin mahaifanta biyu saboda san samun kujerar Sarauta ta tsafi karshe ta faɗi bata cimma nasara ba.

Hakan ya yi matuka bata mata rai ta hakura Samar ya haye karagarta kwatsam Samar ya kawowa Najwa ziyara makaranta anan ya gani tun daga lokacin ya ke nunawa Najwa ta jawoni cikin kungiyarsu hakan zaisa ta zamo Sarauniya idon Najwa ya rufe kwata kwata mulki take so da wannan damar Samar yasata kawoni cikinsu ta hanyar yaudarata ta bani alawa kwatsam na riski kaina a cikinsu.Bangare daya kuma Samar soyayyata ce tai kaka gida a cikin zuciyarsa zuwana cikinsu yafi komai kwantar masa da hankali sai lokacin Najwa ta fuskanta zuciyarta tai zafi saboda tana burin ace itace matarsa kodan ta hau kujerar mulkinsa wnnan yasa ta soma bin wasu matsafa a boye harta kai ga bada jini Nur ya zamo bata da kowa sai Moma hakan yasa ko hutu akai to Jos take tafiya tarkacan tsafinta kuwa na gidansu na Kano fahimtar tsangwamar da Najwa take mun yasa Emeka ta soma taimakamun ta hanyar wani boka dake. garinsu a Ebira cikin dare take tashina mu tafi farkon shigata kungiya naso fita amma suka bani tabbacin mudun na fita zasu kashe mahaifana nikuma du duniya nafisan mahaifana fiye da kowa tsoron hakan yasa naki fita daga cikinsu abinda ya batamun rai na fitinin kowa cikinsu kuwa mutuwar Yasmen hakan yasa na soma yi musu barna nasoma daukar fansa akan Najwa wanda hakan ya haifar mana da gaggarumar gaba uwa uwa tsananin kishin juna. Gagarumar gaba ta cigaba da gudana tsakaninmu sai dai basa nasara a kaina saboda taimakon da Emeke kemun har sukai nasarar kawar da ita bayan ta mallakamun zoban kakanta ta sihiri ni kuma na hallaka Shanny daga nan muketa cudawa har zuwa lokacin aurena".

Murmushi Sarauniyya ta yi tace "kema ba sonki yake ba bibiyarki yake dan cikar burinsa kuma yana daf da cika Allah ya kawo Emeka kika fitinesu kuma ba wata bace Emeka nice Emeka nake bada kama ina bibboyarki duk wani wajan tsafi da kike ganin muna zuwa kawai rufa ido nake miki sabida banaso kisan kudirina a kanki cikin razana Yasiraht ta soma ja da baya tana nunata da yatsa.... wace ce ke?

ku biyomu

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts