New Post

Friday, 7 July 2017

Yar Mafiya... 42-45

[12:54PM, 1/13/2017] Aunty Wawu: *'YAR MAFIYA*
Sanah S Matazu
Rash Kardam
*42*

Take tai murmushi tana dubanta amma kafun tai wani yunkurin magan Najwa ta bace bat bata tashi bayyana ba sai a gidansu ita da Yasar.

Cikin tashin hankali ta soma duba gidan, duk yayi kura alamu sun nuna ta dade a hannun Sarauniya kanta ya sara ta dafe tana tsananin takaci ji take kawai Sarauniya ba bakinsu daya da Samar ta fito kenan ta hangi shigosar yan sanda nan da nan ta bace tazama inuwa tana bin bayansu cikin hirar da suke ta fahimci bincike suke kan gawar da suka riska gabanta ya tsananta faduwa ina Yasar kodai shi aka kashe?.

Take ta bude tafin hanunta tana karanta wasu dalamusan tsafi saiga Yasar kwance a kan gadon asibiti.Hankalinta ya tashi zuciyarta tai na'am data bayyana kanta amma tambayar kanta take ta wace hanya.

Dabara ce ta fado mata ta nufi gidansu,saida ta faki idon mutane ta fadi magashiyan dama ga ciwuka  a jikinta ana nan fa aka zagayeta ana ga Yasiraht kwatsam motar mahaifinta ta nufo hanyar da hanzari ya dauketa zuwa asibiti akai emargancy da ita tana jinsu tai lakur tamkar mataciyya.

Yasar dai jiki sai godiyar Allah kasancewar asibitin suna da kwararun likitoci harya soma bude ido amma baya magana baya gane kowa kwakwalwarsa ta tabu.

Ranar da Yasiraht ta cika kwanaki uku ranar yan sanda da yan jarida suka soma yunkurin san ganawa da amaryar da aka sace a daran tarewa sai gawar maigadi da mijinta a galabaice a ka samu amma da ansoma tuntubarta saitasa kuka hakan yasa basu samu ganawa da ita ba suka hakura.

Da dare ta nemi a kaita taga Yasar,dake babu tazara tsakaninsu babu musu aka yi mata jagora suna shiga sukai sa a Yasar ya farka aikuwa yana arba da Yasirahr take kwakwalwarsa ta soma hautsunawa ya dafe kai yana kara a firgice ya furta.

"Ita ce!  Ita ce!! Ita ce!!!".
Take Samar ya bayyana ya buga masa wani katako suka kwala kara shida ita suka zube a nann...

*Shin  Yasar ya mutu ne?.*

*Ina batun Najwa da Jabir?.*

*Yaya batun Sarauniya?.*

*Shin asirin Jabir Najwa Samar da Yasiraht na tonuwa?. Wake yin nasara tsakaninsu?* .

Sanah
Rash.
[12:54PM, 1/13/2017] Aunty Wawu: *'YAR MAFIYA*
Sanah S Matazu
Rash Kardam
*43*
Nan da nan aka dauki Yasiraht akai bangaran emeegancy da ita,shi kuma Yasar likitoci suka dukufa a kansa binciken farko suka tabbatar da cewar kwakwalwarsa ce ta dawo dai dai amma wani abu ya tsoratashi ta sake samun matsala.

Yasiraht tunda ta farka take matsanancin kuka kamar zata shide Hajiya Yasiraht kuwa ko kallonta batai ba domin tayi zargin da hannunta a kwanciyar Yasar.

Tun bayan bacewar Yasiraht Sarauniya take yunkurin zuwa wajanta, amma babu hali saboda hadarurrukan da take riska a hanyarta.Kamar almara Hajiya Nafisa da Yasiraht na zaune saiga shigowar dan sanda da ankwa hannunsa rike da jaridar data tsoratasu.

Baban shafin Jaridar da aka buga a jiya mai dauke da hotan Baba Maigadi kwance cikin jini sai gefe kuma Yasar magashiyan abin mamaki Yasiraht ce a tsaye a kansu hannunta duk jini. A kasa anyi rubutu da manyan baki kamar haka.

*AMARYAR DA TA KASHE MAIGADINTA TA ILLATA MIJINTA YA RASA RUNANINSA A DARAN AURANSU SABODA WANI KUDIRI DA ITA KADAI TASAN HAKAN AN SAMU HOTUNAN DA SHAIDAR HAKAN NE A HANNUN AMINIYARTA......*

Cikin tashin hankali Hajiya Nafisat tasa kuka,suna ji suna gani aka tasa keyar Yasiraht zuwa kotu Najwa ta kyalkyale da dariya tana gefe tana kallo. Kwata kwata yanzu sun raba hanya ita da Samar da Jabir kowa farautar kowa yake yi.

Tunda aka nufi station da Najwa, mahaifinta yake shige da  fice mahaifiyarta kuwa ta rantse babu ruwanta saboda ga zahiri kowa ya gani bata da abinda yafi mika kai bori ya hau da kyar da sidin goshi ya samu barrister Kurfi ya tsaya musu a shari ar saidai zuwansa uku Yasiraht ta kasa magana sai kuka take karshema tace ya nemamata afuwar mahaifanta ita tasan kasheta za'ayi hankalin mahaifonta yai tsananin tashi duk ya rame addu a ce kawai rake rike da shi ga jikin Yasar rai a hannun Allah.

Ranar Littinin itace aka tsayar ranar shiga kotu, kotun makil take da jama'a babu masaka tsinke nan aka taso keyar Yasiraht tana zubda hawaye nan lauyan gwamnati ya tashi ya gabatar da kansa.

"Sunana Barrister Husssin Abubakar Muhammad, wanda aka fi sani da Brr. HAM ni nake wakiltar gwamnati".

Cikin shigar kamala ya fito yana murmushi, ya shafi kasumarsa zuwa gashin bakinsa.Rash ta taboni "Sanahty wannan gayan fa?" na doke hannunta na sha kunu. "Madam muyi abinda yake gabanmu cikin hanzari ta saisaita kanta nai mata gwalo nace"namiki miji kwalellanki mijin Jiddona ne.Hankalinmu ya koma kansa.

"Sunana Barrister Abdurraham Sulaiman Kurfi, ni ne lauyan dake kare wadda ake kara".

Cikin takunsa mai gamsarwa ya koma ya zauna, nan Brr Ham ya fito yana cin magani.

"Malama Yasiraht ko zan iya sanin dalilin daya sa kika kashe maigadinki da mijinki a daran auranki?".

"Objection ya mai shari a Brr yana neman yiwa wanda ake kara tambaya,mai cike da tozartawa".

"Korafi bai karbu ba".

A sanyaye ya zauna, Brr, Ham yai murmushin mugunta yana duban Yasiraht.

Tana dago kai suka hada ido da Najwa ta nai mata murmushin mugunta a zuciyarta tace "kinyi nasara" a fili ta ce.

"Bani da amsar da zan baka saidai in ce nina kashe shi nima ku kashe ni.. ..".

Kuka yaci karfinta ta kifa kai rana shassheka,mahaifinta ya dinga share kwallar tausayi kamar zaije ya janyota.

Dai dai lokacin Samar na can yana yunkurin zuwa hallatar kotun Jabir ya daureshi tamau habu halin fitowa a tsuburin mula'ali.

Da sauri Barritar Abdul ya mike yace, " ina neman wannan kotu ta daga karar nan har sai an binciki kwakwalwar wadda ake tuhuma"

MUJE ZUWA
[12:54PM, 1/13/2017] Aunty Wawu: *'YAR MAFIYA*
Sanah S Matazu
Rash Kardam
*44*
Haka kotun ta tashi babu wata gamsashiyar amsa, a ranar aka wuce da ita firsin dan jiran hukunci.

Jikin Yasar ya soma sauki an yi sa'ar yi masa aiki kwakwalwarsa ta dawo dai-dai tunda ya farka yaki magana da kowa cikinsu sai bi da ido yanajin yadda suke hira suna aibata Yasirsht mahaifintane kadai baya jin bakinsa.

Sarauniya ta cigaba da bibiyar lamarin Samar da Najwa cikin ikon Allah duk ta karya tsafin da suke takama dashi ta kamasu ta daure.Samar bai mata wuyar kamu ba saboda yana daure a tsuburin muli'ali.

Duk yunkurin Brr nasan ganawa da Yasiraht taki bashi fuska, hasalima in yazo bata sauraransa.Yasiraht ta kade ta rame, tayi baki sossai burinta kawai a yanke mata hukunci ta mutu ta huta.

KOTU ZAMA NA BIYU...........

Kamar yadda aka saba kowane Brr ya mike ya gabatar da sunansa sanan Brr Ham ya soma gabatar da binciken likitoci.

"Ya mai girma mai shari a,binciken likitoci ya tabbatar da cewar Yasiraht lafiyayya ce bata da matsala kota ciwon kai bale tabin hankali.Wannan ya bada tabbacin kisan da tai da nakasa mai gidanta da gangan ta aikata hakan.Ina rokon wannan kotu mai adalci ta gaggauta hukunta wannan azzalumar dan fitarwa da iyalan marigayi hakkinsu".

Cikin girmammawa ya ajiye sakammakon likitocin ya risina yai godiya ya zauna.

"Lauyan wanda ake kara ko kana da magana?".

"Eh ya maigirma mai shari a".

Kamar an keho su suka shigo kotun hakan yasa Brr dakatawa gaba daya kallo ya koma sama.

Samar ne da Najwa cikin galabaitacan yanayi,bayansu Jabir ne yana huci.

"Afuwan ya mai girima mai shari a mun katse muku hanzari amma hakan yana da muhimmanci saboda wadaanan Azzaluman sune silar komai".

Nan take kotun ta hautsine kowa da abinda yake fada, Alkali ya buga abin dakatawa kowa yai shiru.Sannan ya bawa Brr damar magana da Jabir cikin nutsuwa ya dubeshi".

"Malam munasan sanin sunanka da dalilinka da kawo wadsnan bayin Allah kan cewa sune tushan wannan matsala".

Murmushi Jabir ya yi yana dubansa.

"Cikakken sunana Jabir Adama Saulawa,ni haifafan garin Katsina ne sana ata shi ne kasuwanci bani da iyali.Kamar yadda kasani na gaya muku cewa wadanan mutane su ne tushan wannan fitina eh hakane amma zanfi so kuji daga bakinsu".

Barrister ya juya kan Najwa yana dubanta.

"Mallama ya sunanki?".

"Sunana Najwa".
"Shin menene alakarki da wannan shari'a?".

Kai ta sunkuyar kasa tana share hawaye a hankali ta bude baki ta soma bayani.
"Tabbas nayi nadamar cutar da Najwa... ....." tiryan-tiryan ta dinga bayanin tun daga alakarta da Samar da yadda suka ja Yasiraht har zuwa yau.Kotun tayi tsit sai shashekar kukansu da take tashi,kowa na Allah wadai da Najwa da Samar masu tsinuwa nayi masu kuka nayi.

Bsrrister ya dubi"Samar zancan da Najwa ta fada gaskiya ne?".

"Gaskiya ne Barrister".
"Samar mecece hujjarka ta cutar da karamar yarinya kamar Yasiraht?".Yai shiru na tsayin lokaci sannan ya  soma magana.
[12:54PM, 1/13/2017] Aunty Wawu: *'YAR MAFIYA*
Sanah S Matazu
Rash Kardam
*45*

"Gaskiyar magana tun ranar da naga Yasiraht na tuna da burina da nake son cikawa wato zama babban matsafi wanda zai dinga jagorantar Matasan jahar da nake ciki.Sai dai an bani tabbacin bazan samu ba saina kawo matashiyar budurwa mai kimanin shekaru ashirin da daya wadda ranar data cika shekarun za ayi aikin.Tunda aka lissafun yanayin budurwar nake fafutukar nema kwatsam nai gamo da Yasiraht saidai kash shekarunta basu kai ba hakan yasa nasamu nasarar dasawa Najwa son ta jawo mana ita tare da yimata alkawarin hawa kujerar Sarauta.Lokacin da Najwa ta kawo Yasiraht sai nabata sarauta dan san karfafa kusancina da ita hakan ya tunzurata ta soma nunawa Yasirahr tsana da hantara tun bata fahimta ba harta fahimta suka soma takun saka sai dai bata nasara kanta nasararta daya kashe Yasmine da tayi.Sai kuma wannan sharin da taiwa Yasiraht.

A duniya babu abinda na tsana irin ganin Yasiraht da wani namiji hakan yasa na dasa mata tsanar kowa saboda an bani tabbacin mudin nai sakaci ta soma soyayya to aikina zai wargaje Marwan shine saurayin dana fara kashewa sannan na dasa mata bakin jinin dana saurayin da yake kulata.

Daganan ya dora bayanin kaf abinda ya faru bayan shigowarta kungiya har zuwa kashe me gadi da kwanciyar Yasar asibiti.

Ya cigaba...Najwa ita ta hada tsafin da ta hada hotan Yasiraht da gawar maigadi ta taka takaiwa jamian tsaro ba tare da sun gane ita bace tai bada kama ta basu report na komai sai dai sun tsareta a cell dansan tsananta bincike amma da suka dawo babu ita hakan yasa sukaita nemanta amma ko me kamarta basu samu ba tilas suka tattara hotuna da rahotanni zuwa ga yan jarida nan da nan aka shiga yadidi da hotuna har aka kama Yasiraht.Kama Yasiraht ya fusata Sarauniya sossai".

"Wace ce hakan Malam Samar? ".

Lokacin da mukai nasarar shigar da Yasiraht cikinmu bisa sakaci da take da yin addu'a sai Sarainiya ta dinga bibbiyar rayuwarta.Sarauniya wata jinsi ce cikin jinsin aljanu amma musulmace ita take taimawa Yasiraht wasu lokutan tana bibbiyar Yasiraht ne saboda taimakon da mahaifinta ya yi mata a wasu shekaru........ nan ya bada labarin alakar mahaifin Yasiraht da Sarauniya har zuwa dauketa da tayi da godowar da tayi  sanan ya cigaba.

"Wannan ya fusata ta ta dinga bibiyar lamuranmu, fahimtar hakan yasa muka dinga wasa da hankalinta nida Najwa wajan tare mata hanya harta samu kaucewa da taimakon Jabir ta kamamu ta karya duk wani shiri namu harta samu nasarar kawo mu wannan waje".

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts