New Post

ABUBUWA BAKWAI (7) ABIN KULA GA DAN'ADAM

1. Duniyar da za a barta, me ya kawo hadama? 2. Dukiyar da za a lissafa daya bayan daya, me ya kawo tarata? 3. Rayuwar da zata kare, ina wani farin ciki? 4. Yarintar da tsufa zai zo mzta, me ya kawo takama? 5. Ana sauraren mutuwa, ina wata walwala? 6. Jikin da zai zama gawa, me ya jawo dagawa? 7. Karshe dai makomarsa kabari, me zai sa alfahari? Wanda ya manta da wadannan a ina ya bar hankalinsa? Allah yasa mu dace, yayi mana kyakkaywan karshe. Ameen!

KADA KA RAMA CUTA GA WANDA YA CUCEKA!

Kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka, kai kayi hakuri. Zaka samu abu biyu sakamakon hakan; * Na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. * Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

KADA KA BARI ZUCIYARKA TA ZALUNCEKA!

Kada ka sale zuciyarka ta zalunceka, tabbas zaluncin zuciya ga gangar jiki yake komawa, idan akayi wasa ya zamanto ya shafi rayuwa. Assasa bak'in tunani, yawan zargi da rashin tabbas akan wani aiki, zato, shakku ko kokwanto akan wani al'amari batare da tantance gaskiyarsa ba, shine zaluncinzuciya akan dan Adam. Maza ka hana zuciyarka don akwai hadurra dubu akan hakan.

MAHAKURCI MAWADACI

Tabbas ba kowane dandanon magani ne ke da dadi ba, amma babu shakka shine abu mafi dacewa ga dukkan mara lafiya. A lokuta da dama rayuwa takan dakeka da guduma ta jefaka acikin wani mawuyacin hali, kayi ta fama amma tayi maka tutsu. Amma idan kayi hakuri sannu ahankali zata kwaranye. Hakika ba duk abinda rai yake so yakan samu ba, amma bukata bata taba sauyawa ba kuma bata taba karewa ba. Don haka ka shirya bukatunka da kyau ka bisu daya bayan daya sannu a hankali, kayi gwa- gwarmaya, sannan kayi juriya. Tabbas mafarkinka zai zama gaskiya.

KO KA SAN?

Rayuwa bakin alqalami ce tana bukatar kaifi sannan tana son tsini. Kaifin don ka yanki magauta, tsinin kuwa don ka soki makiya. Haka zalika rayuwa kamar randar ruwan sanyi ce ta kasa tana bukatar tanaji da adani, kodn wata rana ka shayar da masoyanka. Da kyau ka lura da abu biyu a rayuwa; 1. Ka lura da mai zaginka mai aibantaka wata kila wata rana zai iya zama masoyinka mai yabonka 2. Ka lura da masoyinka na kusa mai yawan ambaton alkhairinka, wata kila wata rana zai iya zama makiyinka mai zaginka.

Tuesday, 18 April 2017

'YAR MAFIYA....

💀 *'YAR MAFIYA....* 💀

                      *_NA_*

         *_©RASH KARDAM💕_* 
                            _&_
        *_©SANAH S MATAZU💘_*

_لبسم الله الر حمن الر حيم_

*_الله‍م عالم الغيب و الشه‍ادة فاطر السموات ولأرض، رب كل شيء ومليكه، أشه‍د أن لا إله إلا أنت أعوذ بك من شر نفسى ومن شر الشيطان وشر كه، وأن أقترف على نفعي سوءا أو أجره الى ميلم._*

_اللهم صل على محمد و على أزوجه وذريته كما صليت على آل إبرهيم. وباركت على محمد وعلى أزواجه وزريته كما بركت على آل إبرهم، إنك حميد مجيد._

                *_GATARWA_*

*_Dukkan yabo ya tabbata ga Allah. Muna godiya a gare shi, muna neman taimakonsa, muna neman gafaransa, kuma muna neman tsarinsa daga sharrace-sharracen rayukan mu da miyagun ayyuka. Wanda Allah ya shirye shi babu mai b'atar da shi, wanda kuma ya b'atar ba mai shiryar da shi. muna shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kad'ai, babu abokin tarayya gare shi. Muna shaidawa cewa Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa ne. Ya Allah  kayi tsira ga wad'anda suka bishi da kyakyawan kwaikwayo har zuwa ranar kiyama. Kuma ka musu aminci, aminci mai yawa Ameen_*

                  *JIN-JINA*
  
         Ya zama dole mu yaba mu ku tare da jin-jina muku ga k'ungiyar mu mai tarin Albarka *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* ALLAH ya kara kare mana k'ungiayr mu ya d'aukakata tare da Albarka Ameen.

                    *SHARHI*

   _Wannan labarin k'agagen labarine ba mu d'auki labarin wani/wata mukayi amfani dashi ba, in kuma yazo dai-dai da na wata/wani sai anyi hak'uri da hakan._

                   *®NWA*

Pg~*1.*

Doguwar Yarinya na hango matashiya mai jini a jika shekarun ta bazai wuce ishirin da uku zuwa da hud'u ba kallo d'aya zaka mata ka gane tana matuk'ar ji da kanta tamkar 'Yar gidan sarauta, fara ce kuma tana da d'an tsayi sannan bata cika kyan d'aga hankali ba amma tana da gizo wanda duk ya kalleta zata na yi masa gizo, tana da idanu manya-manya wanda in ka zuba musu ido na wani d'an lokaci zakaga suna canza kala, ko da mukayi duba zuwa fiskan ta daga gani tana cikin matsanaci b'acin rai take yanayin hallitarta tasoma canza wa, da gudu ta fito daga falo ta nufi d'akin ta da ke can k'arshen d'akunan k'ofar ta rufe take ta fara wani irin gurnani tamkar namiji zaki wanda yunwa ya dame shi ya fito farauta, cikin tsoro na kalli Sanah na ce"ke kalli yanda takeyi nikam zan gudu don na tsota da ita na fasa kwasan labarin". Wani harara Sanah ta aika min da shi ta ce"dad'i na dake kin fiye tsoro kamar farar kura ba gani a kusa da ke ba? To miye na tsoron?". Hannuna taja mukaje tagar d'akin da ta shiga muka leka, cikin tsoro nake shirin sakin k'ara Sanah ta toshe min baki ko da na k'ara duba wannan Yarinyan ne ke hawaye amma na jini kanta ke firda wuta tamkar an kunan itace da gass, tafin hannuta ma haka yake fitar da wuta kayan jikinta suka canza kala zuwa ja-jazur, cikin murya mai ban tsoro ta ce"Baba mai yasa zakayi haka? Shin kasan hatsarin da ke cikin wannan al'amarin kuwa? Kasan halin da Yasar zai shiga kuwa? Ina tsoron Samar in yaji wanan al'amarin shikenan zaku rasa Yasar". Cikin tsoro Sanah ta kalleni"Rash wai me ke faruwa ne?", ba tare da na bata amsa ba na kamo hannuta muka nufi falo. Muna daga k'ofa mukaji wani dattijo ya na ce ma Yasar "Allah ya maka albarka tabbas nasan bazaka watsa mana k'asa a ido ba". Wanda aka kira da Yasar kansa na duke a k'asa ya amsa da "Ameen Abba" ya sake rusunawa ya ce"ni zan koma gida naga dare ya soma yi". Tsohon nan ya amsa da"to Yasar ka sauka lafiya ka kula". Cikin girmamawa ya fito yashiga motar sa ya nufi gidan sa ko da ya shiga gida muna biye da shi gate(gareji) ya rufe tare da komawa mota ya ja ya kai gun ajiye motoci ya ajiye motar, ya fito ya fara tafiya irin na gaye wanda ke ji da kansa da kuma boko ya shiga cikin falo tare da mai da k'ofar ya rufe ya nufi hanyar matakala, tass! Tass!!  Tass!!! Kake ji k'arar d'aukewar wuta tare da wani irin walk'iya mai had'e da k'ara tare da tsawa aciki wanda ya samu komawa baya da gudu,  cikin jarumta irin na maza ya soma lalub'en hanya dai-dai k'ofar d'akin ya hango haske wanda ya hango takun sawun k'afa zalla da jini ajiki yana bin hanyar da zai bi, cikin hanzari ya juya zai koma sai ganin yarinya k'arama tana tunk'aroshi ta ware hannuta alamar oyoyo, ga idanun ta yana fitar da hawayen jini bakin ta ma na zubar da jini cikinta yana juyawa da ida mutun yake zai na iya hango zalla jinin da ke juyawa a cikinta, cikin kid'ima yarasa baya zaiyi ko gaba yana juyawa ya ga yarinyar na dariya ta b'ace da gudu yayi hanyar sauk'owa daga matakalar benin, sam ya kasa yin addu'a bare daman shi ba gwanin yin addu'a bane(kira ga 'Yan uwa yana da kyau mu kasance cikin addu'a akullum kar muna mantawa fa Annabi ya koyar mu addu'o'i tun daga kan nashiga bayan gida har da na fita a gida dan Allah mu dage baran yanda zamanin nan ya zama).

    Masu karatu ku biyo 'YA'YAN MUTAN;

*KARDAM DA 'YAR MUTAN MATAZU.*

  *RASH KARDAM💕*
               & 
*SANAH S MATAZU*

'YA'YA DA DUKIYA.... LAST PAGE

[10:34AM, 5/26/2016] Rash Kardam :
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-146~150.
Bayan sun dawo, su Gwaggo an dawo
Hajiya, Gwaggo ne ta fito daga unguwa
ta kame abayan mota, dai-dai kwanar
unguwansu, ta hango an taru, wata mata
sai dukan wata yarinya take, da sauri
tasa mai driver ya tsaya, wani ta
tambaya maike faruwa nan yasanar
mata, yarinyar da ake duka yar riko ce,
wai taje tala ta b’atar da naira hamsin
ake dukanta. Da sauri taje ta rike matar
na, tace”haba baiwar allah mai yayi zafi
haka?.
“Akan kd’in da baitaka kara ya karya
ba?” Ko dan kinga bake kika haifetaba?
“Kisani fa ‘YA’YA DA DUKIYA BA’A
K’ETARSU.
nasiha ta mata sosai kafin ta ba ma
matar 500 ta kuma ce karta daki
yarinyan ta tafi.
Bayan kwana biyi Gwaggo na zaune a
gida, taji jiniya kafin ta mike saiga
Khadi tashi da yan ‘YA’YAN TA, da gudu
sukayi gun Gwaggo duna oyoyo grany,
Gwaggo tace”washh yaran nan zaki
karya ni, takali, Ahmad tace”ni yanzu na
fasa Auren da kai ka tsufa, Hafsat”ke
kuma kinyi kwaliya kinzo ki kwace min
miji.
“To baya sonki”
Dariya sukayi gaba d’ayansu, rayuwa
kenan hausawa sunyi gaskiya da
kalmasu ta Mahak’urci mawadaci.
Kira gareku yan’uwa mata, kunga yanda
labarin nan ya kasance akan Gwaggo,
kusani ‘YA’YA ko bana ka bane, kurikesu
tsakani da Allah, bakasan mai tai
makonka ba, bakusan wazakuci
albarkacinsuba. Allah ya bamu YA’Ya na
gari Ameen.
ALHAMDULILAH
Alhamdulilah! Dukkan yabo sun tabbata
ga Allah ubangijin sammai da kassai,
wanda ya bani ikon kammala wannan
littafi lafiya, kuskuren danayi ya Allah
ka yafe min Ameen.
IYAYENA ABUN SONA
Iyayena abun Alfaharina, ina matuk’ar ji
daku
Alhaji Abdullahi Garba Kardam
Hajiya Khadija Aliyu Abfullahi, Allah ya
barmun ku ya ja kwananku Ameen.
SADAUKARWA
Na sadaukar da wannan littafi sukutum
da guda, gareki MUMCY NA Khadija
Alkali(Khadija Candy).
GAISUWA TA MUSAMMAN
Gai suwa ta musamman gareku
yan’group d’in Khaleesat Haiydar
Facebook, da badun karnayi son kai ba
sainace kufi kowa Son wannan novel
d’in, nagode Allah ya bar do da quna.
GODIYA TA MUSAMAN
gareku,
Maryam S Bello
Maryam alkali Mamu(Mrs jabo)
Aishat Muh’d(Maman Shakur) bazan
manta daku ba
GODIYA K’UNGIYAR
EXTREME HAUSA WRITER’S
WISDOMS HAUSA WRITER’S
BEST HAUSA WRITER’S
K’AWAYENA
Godiya ta musamman gareku kawayena
Zee Autar Hajiya
Aishat S Mazoji
Nuceeyluv
Beebah Luv
Zee Hrt
Futha Luv
Sadeeya
My Falmi
Jiddah Ja’o
Mesha Luv
Munay
Kausat Luv
Maman Abideen
Zahrah
Hauwah Jiddah Aliyu
Rabee’at SK Mashi
Amrha Luv
Mrs Umar Soja
Stylish
Zahrah BB
Khairat S Panisau
Sadiya Abdullahi ‘Dahiru
S.A Azeez
Memie Bee
Fulani Cerdiya
Baby Amrah.

'YA'YA DA DUKIYA... 141-145

4:55PM, 5/25/2016] Rash Kardam :
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-141~145.
Shirye-shirye biki akeyi ba sanya, su
Hajiya Jamila.k’irjin biki, su Farhat da
Queen Neena takanas suka koma gidan
Hajiya Suwaiba da zama, abunda aka
shirya za’ayi ran Alhamis kamu, sai
Jumma’a Walima da daddare kuma
dinner, washe gari asabar yini. Komai
ya tsaru yanda ake so, yau ne ranar da
za’a fara Kamu, da yamma ko kwaye sun
shirya, har an kaisu gun jiran isowar
Amarya ake, ba’a dade ba kuwa ta iso
cikin wata lafiyayiyar mota, tun dana
zuba ido ma Khadi kasa d’aukewa nayi,
gaskiya tayi kyau, duk yan guri sai yaba
kyanta suke, taro yayi taro, komai yatafi
yanda akeso, sai kusan shida suka gama
kamu, daga gun gidan, Hajiya Suwaiba
aka sake kaita.
Washe gari akayi walima shima tsaru
daddare kuwa sukayi shirin dinner.
Hajiya Suwaiba ta bada umurni akai
Amarya gidansu daga can za’a wuce da
ita Dinner har a kaita gidanta, wannan
umurnin Mum ne.
Masu karatu in bakwayi bamu guri,
tundaga nesa na hango motoci jere suna
d’eban mutane, sai da aka gama diban
kowa, na hango wata maroon d’in lemo
zeen ta perker, su Gwaggo da’ake leke,
baki tasaki tana kalo, don tunda take
bata tab’a, ganin irin motarba. Nan
akace afito da Amarya Inna Yalwa ce ta
rakota, ohoho sunan wani kalma waishi
sorry!! Masu karatu karkuga Khadi, in
har nace zan iya tsara muku kyan da
tayi, wayana ba zai d’auka ba. A hankali
suka isa jikin motar tashiga, ana tayar
da motan taji an rik’o hannuta, a razane
ta juya Umar ne yaaha kyau.
Koda suka isa gun dinner duk wanda ya
gansu sai ya yaba, haka taro ya kare
kowa cike da murna.
Da safe Malam ya kira Khadi, ya mata
nasiha, yan’uwan Mamanta suma nasiha
suka mata, Gwaggo da k’afarta tazo tana
kuka ta roki Khadi yafiya, Khadi tace”
ba komai ta yafe mata.
Da daddare aka d’au Amarya sai gidan
Umar niko Rash nace”fatan alkairi.
Gwamna gida mai ji da kyau ya bamasu
Malam, yace”karsu d’au tsinke acikin
nasu. Haka ayi suka koma, tsakani Beeba
da Dr Abdul ko wata soyayya ne mai
cike, da qauna sukeyi ma junasu,
Gwaggo yanzu kamar bata gidan don
Albarkacin Khadi takeci.
Kwanaki sun tafi shekaru sun sud’e,
koda naje gidan Khadi na hango ta da
yaranta, sun girma suna gudu ko ina,
Khadi yanzu ta dawo cikakoyar mace
mai aji da kamala.
Gwamna ya biya ma su Gwaggo da
Malam aiki Hajji suka tafi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

'YA'YA DA DUKIYA... 141-145

4:55PM, 5/25/2016] Rash Kardam :
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-141~145.
Shirye-shirye biki akeyi ba sanya, su
Hajiya Jamila.k’irjin biki, su Farhat da
Queen Neena takanas suka koma gidan
Hajiya Suwaiba da zama, abunda aka
shirya za’ayi ran Alhamis kamu, sai
Jumma’a Walima da daddare kuma
dinner, washe gari asabar yini. Komai
ya tsaru yanda ake so, yau ne ranar da
za’a fara Kamu, da yamma ko kwaye sun
shirya, har an kaisu gun jiran isowar
Amarya ake, ba’a dade ba kuwa ta iso
cikin wata lafiyayiyar mota, tun dana
zuba ido ma Khadi kasa d’aukewa nayi,
gaskiya tayi kyau, duk yan guri sai yaba
kyanta suke, taro yayi taro, komai yatafi
yanda akeso, sai kusan shida suka gama
kamu, daga gun gidan, Hajiya Suwaiba
aka sake kaita.
Washe gari akayi walima shima tsaru
daddare kuwa sukayi shirin dinner.
Hajiya Suwaiba ta bada umurni akai
Amarya gidansu daga can za’a wuce da
ita Dinner har a kaita gidanta, wannan
umurnin Mum ne.
Masu karatu in bakwayi bamu guri,
tundaga nesa na hango motoci jere suna
d’eban mutane, sai da aka gama diban
kowa, na hango wata maroon d’in lemo
zeen ta perker, su Gwaggo da’ake leke,
baki tasaki tana kalo, don tunda take
bata tab’a, ganin irin motarba. Nan
akace afito da Amarya Inna Yalwa ce ta
rakota, ohoho sunan wani kalma waishi
sorry!! Masu karatu karkuga Khadi, in
har nace zan iya tsara muku kyan da
tayi, wayana ba zai d’auka ba. A hankali
suka isa jikin motar tashiga, ana tayar
da motan taji an rik’o hannuta, a razane
ta juya Umar ne yaaha kyau.
Koda suka isa gun dinner duk wanda ya
gansu sai ya yaba, haka taro ya kare
kowa cike da murna.
Da safe Malam ya kira Khadi, ya mata
nasiha, yan’uwan Mamanta suma nasiha
suka mata, Gwaggo da k’afarta tazo tana
kuka ta roki Khadi yafiya, Khadi tace”
ba komai ta yafe mata.
Da daddare aka d’au Amarya sai gidan
Umar niko Rash nace”fatan alkairi.
Gwamna gida mai ji da kyau ya bamasu
Malam, yace”karsu d’au tsinke acikin
nasu. Haka ayi suka koma, tsakani Beeba
da Dr Abdul ko wata soyayya ne mai
cike, da qauna sukeyi ma junasu,
Gwaggo yanzu kamar bata gidan don
Albarkacin Khadi takeci.
Kwanaki sun tafi shekaru sun sud’e,
koda naje gidan Khadi na hango ta da
yaranta, sun girma suna gudu ko ina,
Khadi yanzu ta dawo cikakoyar mace
mai aji da kamala.
Gwamna ya biya ma su Gwaggo da
Malam aiki Hajji suka tafi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

'YA'YA DA DUKIYA... 141-145

[4:55PM, 5/25/2016] Rash Kardam :
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-141~145.
Shirye-shirye biki akeyi ba sanya, su
Hajiya Jamila.k’irjin biki, su Farhat da
Queen Neena takanas suka koma gidan
Hajiya Suwaiba da zama, abunda aka
shirya za’ayi ran Alhamis kamu, sai
Jumma’a Walima da daddare kuma
dinner, washe gari asabar yini. Komai
ya tsaru yanda ake so, yau ne ranar da
za’a fara Kamu, da yamma ko kwaye sun
shirya, har an kaisu gun jiran isowar
Amarya ake, ba’a dade ba kuwa ta iso
cikin wata lafiyayiyar mota, tun dana
zuba ido ma Khadi kasa d’aukewa nayi,
gaskiya tayi kyau, duk yan guri sai yaba
kyanta suke, taro yayi taro, komai yatafi
yanda akeso, sai kusan shida suka gama
kamu, daga gun gidan, Hajiya Suwaiba
aka sake kaita.
Washe gari akayi walima shima tsaru
daddare kuwa sukayi shirin dinner.
Hajiya Suwaiba ta bada umurni akai
Amarya gidansu daga can za’a wuce da
ita Dinner har a kaita gidanta, wannan
umurnin Mum ne.
Masu karatu in bakwayi bamu guri,
tundaga nesa na hango motoci jere suna
d’eban mutane, sai da aka gama diban
kowa, na hango wata maroon d’in lemo
zeen ta perker, su Gwaggo da’ake leke,
baki tasaki tana kalo, don tunda take
bata tab’a, ganin irin motarba. Nan
akace afito da Amarya Inna Yalwa ce ta
rakota, ohoho sunan wani kalma waishi
sorry!! Masu karatu karkuga Khadi, in
har nace zan iya tsara muku kyan da
tayi, wayana ba zai d’auka ba. A hankali
suka isa jikin motar tashiga, ana tayar
da motan taji an rik’o hannuta, a razane
ta juya Umar ne yaaha kyau.
Koda suka isa gun dinner duk wanda ya
gansu sai ya yaba, haka taro ya kare
kowa cike da murna.
Da safe Malam ya kira Khadi, ya mata
nasiha, yan’uwan Mamanta suma nasiha
suka mata, Gwaggo da k’afarta tazo tana
kuka ta roki Khadi yafiya, Khadi tace”
ba komai ta yafe mata.
Da daddare aka d’au Amarya sai gidan
Umar niko Rash nace”fatan alkairi.
Gwamna gida mai ji da kyau ya bamasu
Malam, yace”karsu d’au tsinke acikin
nasu. Haka ayi suka koma, tsakani Beeba
da Dr Abdul ko wata soyayya ne mai
cike, da qauna sukeyi ma junasu,
Gwaggo yanzu kamar bata gidan don
Albarkacin Khadi takeci.
Kwanaki sun tafi shekaru sun sud’e,
koda naje gidan Khadi na hango ta da
yaranta, sun girma suna gudu ko ina,
Khadi yanzu ta dawo cikakoyar mace
mai aji da kamala.
Gwamna ya biya ma su Gwaggo da
Malam aiki Hajji suka tafi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

'YA'YA DA DUKIYA 136-140

’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-136~140.
Umar kuka yake ana haka har suka iso
New Delhi, motane tazo ta d’aukesu har
asibitin da za’a mata aiki, kasancewa a
sanar musu, sun sanda suwansu, ana
shiga da ita likitoci, suka hau bata
taimak’on gagawa. Sun d’au awani suna
mata surgery, Umar ya kasa zaune ya
kasa tsaye, duka sun dun kufa sai addu’a
sukeyi. cikin ikon Allah likitan ya fito
cike da fara’a, hannu ya mika ma
Gwamna, yace’ In Allah ya yarda musa
tsamani komai normal”
Hamdalah suka rayi, suna gun akazo aka
wuce da ita zuwa d’akin da zasu ajeyeta.
Khadi bata far-fad’o ba sai kusan
3:00am na dare, doctors aka kira duka
dubata, Umat ko sai addu’a ke mata.
Haka suka kasance cikin jinyan Khadi
yau kusan watandu d’aya kuma yau ne
za’a ware mata, bandage, doctor
yace”suyi fatan Allah yasa aikin yayi
nan aka shiga da ita, wani room don
since mata, su Umar sai addu’a yakeyi.
Awa d’aya ya d’aukesu, likita ya fito nan
ya saida musu komai normal, zasu iya
shiga su ganta, Umar da gudu yayi
d’akin yana zuwa ya ganta kwance, suna
had’a ido murmushi ya sakarmata, zuwa
yayi ya rungumeta, ana haka su Malam
suka shigo, sai da Dad yayi gyaran
murya, tukun ya san sun shigo, cikin jin
kunya ya koma gefe, sannu suka ringa
mata.
Tun daga wanna ranan Umar shike mata
dressing d’in ciwonta, ya bata abinci
abaki, ya mata alwala, da daddare kuwa
kafin ta kwanta zai d’auko story book
yana karanta mata, da joke masu dad’i
tana dariya, har tayi baci, inyaga tayi
nisa da bacci yazo ya ru gume matarsa
haka rayuwansu, ya kasance gwanin
dad’i. Ganin Khadi ta warke suka fara
ahirin dawo 9ja don ayi biki kowa ma
ya huta.
Gwaggo kam taci a zaba, in har kasanta
ada kaganta yanzu bazaka ganeta ba,
tayi baki sosai, gashi har hak’urinta sun
zube, tsaban duka da wahala, sai daga
baya ne, Beeba ta sanar ma Dr Abdul
gaskiya, shima ya fad’a ma Baban Umar,
sai da sukayi bincike suka tabbatar da
gaskiyan al’amarin kafin aka saketa,
randa tashiga unguwansu, matasa suka
tashi zasu mata duka da kyar aka
kwaceta, Gwaggo tayi nadama ba kad’an
ba. Kulum cikin saloli take, tana addu’an
Allah ya tashi kafad’un Khadi.
Yau jirgin su Khadi ya sauka 9ja, Umar
ko sai wani rawan kai yakeyi, ko
kunyasu Dad baiji, sai yawani rok’o
hannuta, sai da Mum ta zo ta rik’e
hannu yarta, Mum tace”Malam za’aban
aron yata, zan tafi da ita kafin biki.
Yace”bakomai ae Khadi takune.
Suna isa gida ta kira Hajiya Suwaiba da
Ameena tace”ga yata nan kuje a gyara
min ita, banson Umar ma ya ganta sai
biki.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

'YA'YA DA DUKIYA.... 126-130

[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-126~130.
Hajiya Suwaiba suna komawa, suka
sanar da Mum d’in Umar yanda sukayi,
tayi mamaki sosai ashe da gaske haka
halin Gwaggo yake. Nan tace” hmm ni
gwanda His Excellency ma ya dawo ayi
bikin, yarinya ta huta.
Hajiya Suwaiba tace”yaushe zai dawo?
Mum tace” nan da 5days zai dawo. Hira
sukayi tayi da yanda biki zai kasance.
Gwaggi ko ta hana su Malam bacci sai
ihu take, ko sallah anki bud’eta tayi.
Khadi tayi murna tayi godia ma Allah da
zab’in da ya mata, take ta kira su Farhat
B Haske ta fad’a mata, Farhat ma take
bata labarin tayi sabon saurayi, Sunansa
Abdul-wasilu Humble, Khadi ta mata
fatan Allah ya dai-daita su.
Tana kashe wayar ta kira Queen Neenah
ita ta fad’a mata, daga nan takira Hajiya
Jamila Abubukar ta sanar mata, tayi
murna sosai da sosai, takuma bata
shawarwari da yanda zata kula da Umar
kasancewa Hajiya Jamila ta girmesu,
tana kwance dasune don taga suna da
hankali shiyasa.
Malam ganin iskanci Gwaggo zai wuce
gona da iri, da safe yaje ta windoq duk
ta wargaza d’akinta, yace”Hauwa ki
nutsu, wallahi kinji na rantse, matsawan
baki bar haukan da kike ba to yau zan
rubuta miki saki, don ba za’azo biki ina
matsayina na Surkin Gwamna a ga
mahaukaciya a gidana ba, kuma
haukanta akan bakincin take ma Surkan
Gwamna. Ni Rash nace”hmmm Malam
da biyu yayi maganan nan, don ya kuna
Gwaggo ne.
Gwaggo tace” eh dole kace haka ae dama
baka sona don yanzu kaga Khadi zata
auri d’an Gwamna dole kamin haka.
Malam yace” kene bazaki gane ba ina
sonki sosai, halinki ne bana so, ya fita
abunsa.
Gwaggo jin saki ta nutsu ko da tafito,
jummai k’anwarta tayi mata nasiha
tace”Yaya matsawan baki kwantar da
kai ba, ina fad’a miki zaki wahala don
yarinyan nan tayi gaba. Kiyi hak’uri
kawao.
Gwaggo tundafa wannan rana ta dawo
kamar bata gidan yanzu bata dai
magana da Khadi, amma ta bar
hantaranta ko sabganta tabar shiga.
Khadi ko kulum suna mak’ale da waya
ita da Umar, suna waya ne yace”gobe
Dad zai dawo ki shirya, in ya dawo ke da
Beebah zakuzo ku gaidashi.
Cike da murna tace”sai mun tambayi
Baba in ya barmu.
“Kedai nasan Baba bazai hana kizo ki
gaida Surkinki ba. Haka sukayita
hiransu mai cike da ni shad’i.
Washe gari da safe inna ta d’aura ruwa
a hita, dai-dai kusa da d’akinta a kwai
soket, ya tafasa ruwan ta kashe, taje
d’auko boket kenan ta sukuya tana
d’aurayewa, sai tebur d’in ya karye yana
shirin zubowa akan Gwaggo.
Khadi tafito da ga d’aki karaf idonta ya
sauka akan tebur, “kira ta kwala ma
Gwaggo, ganin bata gane mai take nufi
ba, da sauri tayi gun don ceton Gwaggo.
Tana zuwa ta ture Gwaggo ta hantsula
gefe kagin ta kauce ruwan ya juye mata
ajiki, wani razanane k’ara tasaki, ta
fad’i agun tana shure-shure. Gwaggo duk
ta rikice, Beeba da Rabee sai Jimmai
kanwar Gwaggo suma ihu suka saki, ana
haka sai ga Mal da gudu yayi kan Khadi,
wanda azaba yasa ta suma, d’aukarta
yayi waje yafita da gudu yashiga Napep,
Gwaggo ma da gudu duka bisa, Beeba
kam sai kuka take, tana fad’i”wayyo
Adda na!. Gwaggo sai hawaye takeyi,
tabbas yau Khadi ta gwada mata yar
halak ce ita, gashi taje ceton rayuwana
itakuma zata rasa nata. Tabbas yau na
yarda da kalman nan ta ‘YA’YA DA
DUKIYA BA’A K’ETARSU, bakan wanda
zai tai makeka ba.
Suna isa asibiti Dr Abdul suka samu
gani halin da take ciki, akayi Emergency
da ita, wayan Dr Umar yakira.
Dr Umar suna Airport shida Mum da
Ilham sunje d’auko Dad d’insu, don har
jirginsu ya sauka, Dad ya sauko kenan,
sun rungume juna, wayar Dr Umar tayi
k’ara gani Dr Abdul yasa yad’aga da
sauri “hello yace”.
Daga d’aya ban garen Dr Abdul
yace”kana ina, kazo ba lafiya Khadijat ta
kone bansam ko garin yaya bane, amma
ina zati ko Gwaggo nane ta konata
sabida halinta.
“What ina bazai yuba sai na d’au
mataki.
Mum tace”Kai da wa?.
Cikin muryan kuka ya fara basu bayani,
His Excellency yace” what muwuce
Asubiti yau matan na zata gane ita
bakomai bane.
Suna zuwa Asibiti ta ko ina ya amsa da
jiniya.
Dr Umar da Gwamna da gudu suka fita
duka shiga Emergency, Umar na ganin
halin da Khadi ke ciki, kara ya saki ya
fad’i sume. Mum da Ilham sai kuka suke,
Gwamna ya fita kiran Doctors suka d’au
Umar shima. Yana fitowa yaga su Malam
yace”ina Gwaggo da take?.
Malam ya nunata da yatsa, His
Excellency da gudu yayi kanta wani
damka ya mata, ya fara kwara mata
kyawawan mari, yace”wallahi in har na
rasa d’ana d’aya tilo, da abar qaunar sa,
to kema sai kinyi mutuwar wula kanci.
Kisani ‘DA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU.
amma ke munguwa nai bakin hali zaki
gane kurenki. Ball yakeyi da ita, yana
fad’an magan ganu, da kyar aka rik’e
shi, sijoji yace atafi da ita CID agana
mata azaba. Basu tsaya jiran komai ba
Women police suka d’au Gwaggi sama
aka sata a mota, aka nufi CID da ita.
Ni ko Rash tsaban gulma ina leka motar
naga bakin Gwaggo har ya kun bura,
fiskan taji marin manya, tamkar ba
Gwaggo mai bala’i ba.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:

'YA'YA DA DUKIYA.... 121-125

’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-121~125.
Gwaggo ta buga k’irji tace”nashiga uku,
anya kuwa ba Khadi mu bane.
Matar tace”nan gidan mana”. Innna
Yalwa tace”sannuku da zuwa ga gurin
zama”. Cike da fara’a suka k’ara
shigowa. Nan fa aka shigo da akwatuna,
ko da aka shin fud’a taburma, hmm
akwatuna bazai yiwu a bazasu, a tsakar
gidan ba. Inna Yalwa tace”yan’uwa yana
da kyau, kafin mu fara bud’e kaya, muyi
addu’a Allah ya sanya alkairi, ya kad’e
fitin-tinun dake ciki, ya kuma kawar da
idon mahassada da makiya, dazasu kawo
farmaki ma auren nan. Gwaggo tace”kee
Yalwa wa zaiyi hassda ko makiyi nasan
dani kikeyi, nan Gwaggo ta fara kwala,
ko ta kanta basu bi ba, sukayi addu’a
aka fara bud’e kaya. Yasalam masu
karatu karkuso kuga kayan yawanci
ready made ne, ga tsada, ko da ka zo kan
takalma duk gulma na, na kasa k’irga
yawansu, jakukuna da poss ba’a magana.
Ko da aka bud’e na d’ankunaye hmm
gwala-gwalai da fashion masu tsada, ga
manyan balguls ba a cewa komai, can
idona ya kyalo wani karamar a kwati
acikin kayan, da sauri Inna yalwa ta
d’auko, tayi-tayi ta bud’e amma ta kasa,
wannan matar ne tace”kawo ki gani,
tana tab’a qofar akwatin yafara k’ara
sauti mai dad’i gashi da k’arfi. Tana
bud’ewa yace Hello My Master, cikin
wata tausasashiyar murya na mata, kai
ka d’auka a fili mutum yayi wannan
maganan ba.
Wata mata da ke gefe, tace” a kula da
wannan a kwatin, don White Gold ne a
ciki, yana da matukar tsada sosai,
kud’insa ya kai miliyan uku a kud’in
9ja. Inna Yalwa baki har kuni godia suka
fara musu, sai suka d’auko d’an kayan
da suka had’a musu suka mik’a. Inna
Yalwa da dubu biyar a jikinta, ta k’ara
musu yadawo 15k. San suki karb’a sai da
su Inna Yalwa sukace”ko kun rainane?.
Da fara’a sukace”a’a Allah ya sanya
alkairi, wane mu da raina kyautan da
zata fito, daga gidan surkan Gwamna,
matar d’ansa d’aya tilo. Inna Yalwa
cikin rashin fahimta tace” umm Hajiya
bam gane kince Surkar Gwamna ba?.
Matar tace” eh ko bakusan cewa Umar
shine d’an Gwamna d’a d’aya tilo na
miji.
Inna Yalwa tace”sam bamu sani ba ya
ma b’oye mana ko shi waye”.
Take matar ta war-ware musu, aikafin ta
rufe baki. Gwaggo tasaka ihu ta hau
tsakiyar kayan tana watsi da su, tana
cewa” wanna fa k’arya ne d’an yankan
kai ne, Hajiya Suwaiba k’anwar Adam
Naira cike da mamaki, tace”lalle tabbas
yau naga halinki da’ake fad’a.
“Bari kiji ga kayan Lhadijat nan abu
d’aya ya bata sai mun miki rashin
mutunci, kisani duk wanda zakana masa
hassada da bak’in ciki, Allah kan masa
sakayya, mugunta da kike mata ne Allah
ta bata. Gwaggo tayi kanta zata
cakumeta wani security ya kaimata
naushi ta fad’i a kasa. Hajiya Siwaiba
tace”ae da ka barta da yau na koya mata
hankali, ni ba irin matan da suke
d’aukan wargi bane.
“Mtsss bamza sakarya marar imani.
“Khadijat takusa hutawa da muguntanki.
Gwaggo na ihu kamar mahaukaciya,
tana cewa”sai kun kawo na Beeba da
Rabee’ in ba haka ba zamana lafiya.
Gwaggo hauka tuburan Inna Yalwa ta
kali K’anwar Gwaggo tace”da fa kin
kama yar’uwanki kartayi tsirara, tsabam
bak’in ciki. Da kyar aka shigar da
Gwaggo d’aki aka kule ta.
Malam da yadawo, ko da yaji labari,
Hamdalah yayi, ya k’ara gode ma Allah,
tabbas Khadijat ta samu miji, don yana
jin labarin halin d’an Gwamna. Kayan
yasa ka aka d’eba a gidan aka kai gidan
Inna Yalwa da daddare, ba wanda
yasani, motar kuwa ya kai gun wasu
masu ajiye mota aka ajiye masa.
Yan’unguwa ko ina ka leka sai zance
akeyi, wasu ko so suke su ga Khadi matar
d’an Gwamna.
Gwaggo tana d’aki sai zage-zage take,
Beeba ko murna ba’a magana.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:

'YA'YA DA DUKIYA..... 116-120

’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-116~120.
A gidan su Dr Umar kuwa, sun gama
had’a lefe nagani na fad’a, lefen nun ma
sa’a. Cikin kayan harda key d’in mota,
k’irar Honda CRV, Mum d’insa ta saka
masa, Dr Umar shima ya karo wasu kaya
aka saka, masu karatu kar kuso kuga
kayan akwatina ma Set hud’u akasa,
zannuwa kuwa ba kananu. Hmmm
kayan d’an Gwamna d’aya tilo aidole ya
zama abun kalo, Mum tace”Umar ka
sanar da Khadijat jibi za’a kai kaya.
Cikin murna ya shirya sai da ya je Store
ya mata sayya, ya nufi gidan, bai wani
b’ata likaciba ta fito. Sai da sukayi
hiransu yace mata”My Khady!”. Cikin
sanyin murya ta amsa da “na’am”.
“Khadijat! Duk wani farin ciki na kene,
ina matuk’ar qaunanki.
“Alhamdulilah! Allah ya amsa min
addu’a ta, na bani ke amatsayin mata.
“Ki sanar da mutanen gida, In Allah ya
kaimu jibi za’a kawo kayan lefe.
Cikin jin kunya ta saki murmushi, tare
da rufe fuskanta da tafin hannun ta.
Hira sukayi mai cike da so da qauna, sai
dab magriba, ya mata sallama ya tafi.
Khady na shiga gida ko da Malam ya
dawo, bayan ta masa sannu da dawowa,
ta sanar masa da sak’on Dr Umar. Cikin
farinciki ya yi musu addu’a.
Washegari Malam ya aika ma dangin
Mahaifiyar Khady, dangin Uba ya sanar
ma wayanda yakama ta su zo karban
kaya.
Malam ya sayo kayan karban bak’i,
harda yan kajin sa, guda biyar ya tura
kasuwan kauye, aka sayo masa. Ya sayo
multina da lakacera, kaya iya na talaka,
Baba Yalwa k’anwan Maman Khadi su
suka soya kaji, pepper meet sukayi, yayi
kyau ko ina sai kamshi yakeyi. Gwaggo
in banda harare-harare ba abinda
takeyi, ko hannu bata samusu a aiki ba,
karfe uku sun gama komai sun gyara ko
ina sai kamshi yakeyi. Malam yaje ya
d’an had’a kud’in da zai had’a na kasan
akwati, ganin karamci irin na Umar ya
samo dubu goma yaba ma Inna Yalwa
yace a basu. Khady ko tayi wanka cikin
kayan ta masu kyau, suka zauna a d’aki
ita da Beebah don basa son yawo.
Rabee’atu kuwa tana kusa da Gwaggo,
sai lashe baki takeyi, don tunda taga ana
soya kaji, yawunta ya kai.
Su Inna Yalwa wanka sukayi, suka saka
kayan su, mai kyau, suna zaman jiran
baki.
A gidan su Dr Umar kuwa, Mum kwanta
ta kira da matan Baba Liman, sai
Kwanwar Baban su Umar, bata tara
mutane ba, sabida tasan yanayin gidan
su Khady, kar suje su musu ba dai-dai ba.
Milasalin karfe hud’u da rabi, suka d’au
hanyan.
Misalin karge biyar, cikin unguwansu
Khady, ya d’au jiniya, motoci ne sukayi
jerin Gwano ga securitys a motoci sun
sanya sauran motan a tsakiya, suna
shigowa take suka fir-fito dan gani mai
zai faru. Motocin qofar gidan su Khady
suka tsaya.
Gwaggo dake d’aki taji jiniya mota,
tace”ko lafiya naji karan motar yan
sanda?.
Rabee tace”ai inaga wanda suka daki
Adda Khady ne suka dawo dukanta hala.
“Don ranan da irin wannan suka zo.
Gwaggi tace”Allah yasa sune, su dakata
inga ta inda za’ayi auren.
“Zo mu fita muga ya zasu kare. Suna
fitowa dai-dai lokacin yan sanda suka
shigo gidan da bindigansu, Gwaggo sai
zare ido take. ana haka suka ga wasu
Mata cikin shiga ta alfarma sun shigo.
Gwaggo tace”lafiya dai naga kuna shigo
mana gida?.
Wata mata mai yar kiba tace”nan ne
gidansu Khadijat?.
Gwaggo tace”eh! Nan ne.
“Lafiya dai?.
“Lafiya klau, kafin tayi wani magana
ansoma shigo da akwatuna.
Gwaggi tace”wanna fa?.
Matar tace”kayan Khadijat muka kawi”.
Gwaggo ta buga k’irji tare da zaro ido.
Nima Rash sai da wayata ta subuce don
na tsirata da ganin yanayin Gwaggo.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:

'YA'YA DA DUKIYA.... 111-115

YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-111~115
Aiki sosai tayi, Gwaggo tana fita
makwabta, Beeba ta fito tafara tayata
aiki, Khadi tace”Beeba da kin bari nayi,
yanzu in Gwaggo tazo ta samemu, ni
zata zaga uwa ta uba. Beeba tace”karki
damu Adda yanzu zamu gama aikin,
Rabee’a ta fito sai mika takeyi, alamar
daga bacci ta tashi, kitchen ta wuce ta
duna tukunya, taga an kusa gama abinci,
kwano ta d’auko ta d’iba. Beeba
tace”Rabee wani irin iskanci kikeyi ne,
kina kalo muna aiki amma kizo ki d’ibi
abinci?. Baki ta murgud’amusu, Khadi
tace”kyaketa Beeba, kinsan Gwaggo na
dawowa saita huce a kaina. Aiki sukayi
cikin ikon Allah dake, duna da zafin
nama basu dad’e ba suka gama. Khadi ta
raba musu abin ci suka ci, Gwaggi na
dawoa tayi mamakin yanda Khadi ta
gama aiki da wuri, d’aki tashiga kwano
ta fito da shi, ta turo ma Khadi ga
wannan masaran kina gama cin abimci
ki surfa min shi, don yau surfen hannu
nake so bana inji ba. Cikin girmamawa
tace”to Gwaggo”.
A gajiye tayi surfe ta gama ta wanke ta
shanya shi.
Yau takama jumma’a yau ne su Hajiya
jamila da Queen Neenah zasu zo, yan
kud’in da ke Hannuta ta had’a ta siyo
kaya ita da Beeba sukayi girki. Ware
dubu biyu zata basu kud’in Napep, ta
gyara ko ina sukayi wanka ita da
Beebah, sunyi kyau sosai. Gwaggo na
ganin Khadi ta fito tace”mayya inda
kinga fiskanki da bazaki na yawo cikin
mutane ba. Rabee ta mata kalon sama da
kasa, sa’a d’aya Gwaggo bata sasu aiki
ba. Sai kusan karfe biyar, su Farhat suka
kira waya, Khadi ta d’auka da
“sallamanta kun isone?.
Farhat tace”eh! Gamu a dai-dai gun fire
servise”.
“Ok gani zuwa”.
Ita da Beeba suka fita, suna zuwa
kuwata gansu, da murna suka tari juna,
farhat tace”ikon Allah yau Allah yayi
zamu gana.
“Eh wallahi sannu ku da zuwa.
Su hajiya Jamila tace”wanna itace Beeba
ko?.
Khadi ta amsa da”eh! Itace, har kin
ganeta.
Suna hira suka shigo da sallama.
Gwaggo ta musu kalon sama da kasa,
Khadi ko sai addu’a takeyi, d’akin suka
kai su. “Gwaggo ta kwala ma Khadi kira”
ta amsa da “na’am gani zuwa”.
“Kee dan uwarki ina kika samu wayan
nan?. Ko maitan ki ya dawo har gida
kike lashe mutane?.
“Kiyi hak’uri Gwaggo kawaye nane fa”.
“Eyeh har wani daman kawaye kika
samu”.
“To yau zaku ci ubanku daga ke har
kawaye”.
“Dan Allah Gwaggo kiyi hak’uri ki bari
in sun tafi kimin duk abunda kikeso”.
“Kee ko uwarki bazata ban doka nabiba,
bare kee yar karamar kwaro”.
“Assalamu’alaikum Malam yayi sallama”.
“Khadi ta amsa”
Yana daga qofar d’akinsa
yace”Khadejatu! ”
Ta amsa da “na’am Baba”.
“Maza kizo nan”
Gwaggo cikin takaici ta ja tsuka. Sam
bata so haka ba, taso saita wulakanta
Khadi Malam ya dawo.
Da sauri Khadi ta nufi gun Malam, da
sallama tashiga d’akin, tsugunawa tayi
tace”sannu da dawowa Baba”
Cikin fara’a ya amsa da”yauwa d’iyata,
naji dad’in ganin ki, a cikin wannan
yanayi”
“Ya jinin yau fatan lafiya ko?.
“Eh! Lafiya lau, ga kwayena ma sun zi
gaida mu yau”.
“Ah madalla mun gode, in zasu tafi ki
fad’amin”.
“To baba”
Da Murna tayi d’akin ta nan tayi sannu
nasu Hajiya Jamila, Beeba ko har tayi
serving d’insu.
“Tace muje ku gaida Baba na” dukansu
suka mike har qofar d’akin Malam
sukaje suka gaida shi, ya sanya musu
Albarka. Gwaggo ma tafito daga d’aki
duka k’ara gaidata. A dakile ta amsa,
suka koma d’akin Khadi, hira sosai
sikayi, kafin suka mike zasu tafi don
magriba yayi. Ta d’ibi kayan kwaliya, da
sabulai, acikin wanda Dr Umar ya kawo
mata, da turaruka tasamusu a laida. Sun
fito Malam ya kirata yace”ga wanna
kibasu su hau adai-daita. Ta karba ta
“sukuma sukayi godiya”.
Har bakin titi suka rako su ta mika musu
tare da musu alkawarin zata zo ita da
Beeba.
Bayan kwana biyu Khadi na zaman
hak’uri, kulum da kalan horon, da
Gwaggo ke mata. Ana haka kwanwar
Gwaggo da yaranta suka zo mata kwana
biyu, kulum cikin kunci da matsi take,
itaji sanyi to tana tare da Malam ko
Beeba ko Dr Umar.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:

'YA'YA DA DUKIYA..... 106-110

:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-106~110.
Gwaggo ta sha kwalan malam sai ihu
takeyi, ya sa hannu ya ban-bare rigansa,
yazo zai wuce ta sake shan gabansa,
“yaufa bazaka fita agidan nan ba, yau
saika kawo ma Beeba miji. Ya matsa
tabisa yazo zai shiga d’aki ta tare qofar,
sai ya tureta yazo fita ya iso zaure, tazo
da gudu ta kama rigansa saida ta yaga.
Ran Malam in yayi dubu ya b’aci bai san
lokacin da ya kikifa mata mari ba, ya
hankad’ata ta fad’i akasa. Yace”Hauwa
hassadakin bazaikai ki ko ina ba,
wannan aure matsawan in ima raye ba
fashi, sai dai ki mutu da bakin ciki. Ya
juya ya nufi d’aki ya canza kaya, yazo
ya wuceta, har ya fita ya dawo
yace”kuma wallahi in kika kuskura kika
tab’a Khadija, a bakin aurenki saki zan
miki ba dawowa, kina dukanta kin san
sauran, Yasa kai ya fita. Gwaggo abun
duniya ya isheta, tabbas Malam tun da
ya rantse sai ya aikata, jiki ba kwari ta
koma d’aki tafara kuka, cikin zuciyarta
ko cewa take”wanna mari ba zai sha
banza ba tunda yace karna daketa, to ae
dole tayi aikin gida, dan haka ba duka
akwai zagi da wahala yankuma.
Khadi tana d’aki kwace, tana group chatt
da kwayenta, wanda suka had’u a
WhatsApp ta lura suna da hankali,
shiyasa nasu yazi d’aya. A group d’in
Khaleesat Haiydar suka had’u na
Facebook dake Khadi mayar karatun
novel ne. Hiran Novel d’in KAINE SIRRI
NA littafin Aisha Muh’od, Queen Neenah
tace” Khadeejat kin karanta KAINE SIRRI
NA? khadi tace”eh ina karantawa kai,
gaskiya novel d’in ya had’u. Farhat B
Haske tace” Queen Neenah n Khadeejat
kun karanta MARTABA TA da MATAR
MUTUM na Mrs Umar Soja kuwa?.
Sukace “a’a bamu karanta ba.
“Lalle an barku a baya ni harna gama
karantawa, yanzu ina karanta YAR
WAYE NE?.na Khairat S Panisau, da
KUDAN ZUMA na Zee Hrt.
Suka had’a baki tare da cewa”Farhat
littafin ya had’u ne?.
“Eh kai ana rikici kam, ku tamabi.
Hajiya Jamila Aliyu Haiydar tana dashi
sai ta tura muku.
Queen tace”Khady bari na nemomana
zan tura miki ina samu.
Khady tace”ok amma fa nagode. Farhat
B Haske tace”gaskiya ya kamata yanda
muka saba musan juna, gashi mun shaku
sosai, ae zumuncin bai kamata ya tsaya
a chatt ba.
Queen Neena tace” ae fa gaskiya kam,
yanzu musa rana sai mu fara zuwa
gidansu Khady.
“Ko ya kuka gani yan’uwa?.
Duka suka turo da haka za’ayi. Khadi taji
dad’i amma tana tunanin yanda zasu zo
Gwaggo zata iya cin musu mutunci.
Salama sukayi akan ran Friday za’a
had’u, a gidan Hajiya Jamila Aliyu
Haiydar sai su taho.
Gwaggo tana gama sake-sakenata tafito
ta kwala ma Khady kira, “fito dan
ubanki, mai fiska kaman na biri, kin
lashe wa mijina zuciya kin rabani da
yata, gashi kin samu d’an mutane, kinsa
yayi sata sun kawo kud’in aure ko?.
“To ni kam dai ahir d’inki.
“Kurwata kur bazaki iya ci ba.
“Ko uwarki ma haka tagaji ta barni don
nafi k’arfinku.
Nan take idon Khadi yaciko da kwalla.
Gwaggo ta tattaro wanke-wanke ta tara
mata, tashiga d’aki ta d’ebo kaya harda
wankaku, duk ta had’a mata.
“Maza-maza kiyi ki gama su yanzu, ki
kuma tabbatar an girkan abicin kar yayi
dare.
“Kin san halina basai an fad’a maki ba
aha.
“Ni ce Gwaggo Munguwa No1, in kika
kuskure min a aiki sai na miki ba dad’i,
tsohuwar mayya kawai.
“Mai son raba aure, amma kuma bazaki
iya ba sai dai a fasa naki.
“Kuma ina kan bincike duk randa na
gano gidan saurayinki, sai naje na had’a
duk wata manakisa ta, an fasa auren.
Niko Rash”nace Gwaggo rashin sani yafi
dare duhu, da kimsan Umar d’an waye
da baki fara masa rashin mutunci ba,
don yafi k’arfin raini.
Khadi ta dunkufa aiki baji ba gani, duk
da ta gaji amma bata son ta nuna bare
Gwaggo ta zagi iyayenta, don yafi komai
cin mata rai.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:

YAYA DA DUKIYA..... 101-105

’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-101~105.
Cikin takaici ya fincike rigansa, kalon
tsana yake mata, da sauri Gwaggo ta sha
gabansa, yau fa sai na tona muku asiri.
Wani mugun kalon da ya aika mata,
yasa Gwaggo bashi hanya, Khadi da gudu
tabar gun. Gwaggo ta ga kayan da Dr
Umar ya kawo da rawar jiki ta d’iba tayi
cikin gida.
Beeba na ganin haka tace”Gwaggo mai
yasa keke ma Addah Khadi haka?.
Gwaggo cikin zumud’i tace”kee bari
kawai ae ido da ido na kamasu suna
iskanci, cil da cil ganin annabin
tsohuwa. Beeba tace”kai Gwaggo gaskiya
Adda Khadi bazatayi haka ba, zata taba
zubar da mutuncinta ba, kuma na yarda
da tarbiyan da Malam ya bamu. Cikin
b’acin rai Gwaggo tace”oh to! to! Wato
Malam shi ya kula da tarbiyan ku bani
ba?. Beeba shiru tayi ganin Gwaggo ta
d’au da zafi.
Malam na dawowa Gwaggo da
munafurci tazo ta fara labartawa
Malam, Malam ya kaleta sama da kasa
yace”tashi ki ban guri bana son gulma, a
yanzu a kwai wani abunda zaki fad’an
na yarda, bacin nasan irin tsanar da
kikayi ma Khadija, yarinyan mai
hankali, bataji ba bata gani ba, kna
gallaza mata, jiki ba kwari Gwaggo ta
bar d’akin.
Dr Umar ko hankalisa kwance ke
gudanar da aiki, yanzu Dad d’insa kad’ai
ake jira a kawo sadaki, sai asaka ranar
biki.
Sakeenat kuwa sam Mum d’inta, taki
goya mata baya. Hankalinta duk ya
tashi, can ta tuno wata shawara, Zuly ta
k’ira a waya. Tace” kqwara kina ina ne
yanzu?. Zuly tace”gani a hanyan zuwa
gidan ku. “Ok sai kin iso. Ta ajiye wayar
tana zaman jiran zuwan Zuly.
Ko da Zuly tazo bayan ta gaisa da
Hajiyar Sakeenat, tashiga gun Sakeenat,
bayan sun zauna Sakeena tace”kawa
nifa bazan share mari da Umar ya
minba gaskiya. Zuly tace”wani mataki
zaki d’auka?. Sakeenat tace”na bayar a
sayo min dorina hud’u masu kyau,
zamuje unguwansu ba tare da securitys
ba, in munga yarinyan ko mu aika tazo
sai mu cazata.Zuly tace”good idea, haka
zamuyi.
Key motarta ta d’auka suka fita,nan idi
security ya kawo mata sak’onta, ta karba
suka ja mota sai Dakata.
Sun dad’e a unguwan Khadi bata fito ba,
can da suka gaji yaro suka tura yaro ya
kirata, Khadi ko kamar bazata fito ba,
amma can da yaron yasake dawowa, ta
d’au hijab d’inta tace”Beeba ana kira na
a waje barin duba ga wayata nan. Khadi
na fitowa yaron yace”gasu can a wancan
motar. Khadi tana ta raba ido, don Umar
bai tab’a zuwa mata da irin motar ba.
Sakeenat ko suka rike bulala kowa ne
bibiyi a hannusu, sai da Khadi tazo kusa
suka bud’e motar atare, suka nufota da
gudu dukanta suke tak’o’ina. Khadi ihu
take amma basu kyaleta ba, Beeba taji
kamar muryan Khadi da gudu ta lek’o
ganin ana dukanta, koma gida “Gwaggo
dan Allah kizo, yaran ranan suna dukan
Adda Khadi, Gwaggo tace”ha da gaske
Beeba tace”eh!.
Duka suka fito da gudu. Dukanta ko suke
Gwaggo ta fara kukara mata, kunyi min
dai-dai. Rab Beeba ya b’aci sosai, ganin
ba mai ceton Khadi, gashi ba maza a
gun, yasa ta tuna da Dr Umar. Da sauri
ta duba call history, ta kira number,
bugu biyi yad’aga, “hello hello Ya Umar
kazo ga wasu na ta dukan Adda Khadi,
wanda suka zo ranana. Cikin figici
yace”what suwaye?. Kashe yawar yayi
ya shiga mota gudu yake kamar zai tashi
sama.
Sakeenat ko ganin sun mata lilis, ga
mutane sun soma taruwa da gudu suka
shiga mota, suka bar unguwan.
Dai-dai zasufita a layi motar Dr Umar
yadanno kai ganin motar Sakeenat yasa
yasha gabanta, ganin zai tsaresu yasa
taja motar da k’arfi sai da ta buge masa
glass d’in mota ta gudu. Da har zai bita
sai ya tuna kowani hali Khadi take
kuma?. Sai ya fasa ya kara gudu.
Beeba ko ganin sun tafi dakyar wata
makwabciyar su, ta taimaka mata suka
shiga da Khadi gida. Karkuga fiskan
Gwaggo fal farin ciki.
Dr Umar na zuwa yaga mutane, da gudu
yayi salama ya shiga gidan, Beeba ya
fara karo da ita cikin damuwa ke
tambayrta ina Khadija?. Hawaye ya
k’ara zubowa “tana d’aki a kwance.
Yana shiga yaga halin da take ransa ya
b’aci sosai. Ya kira beeba yace” ki had’a
ruwan zafi don tayi wanka, waya ya
kira ba afi minti goma ba sai ga wasu
ma’aikatan asibiti da kaya, da kanta
yamata treatment, ya mata allura nan
take bacci ya d’auketa. Yana fitowa
yace”sistet Beebah barinje gida na dawo.
Na mata allura ta samu bacci, in ta tashi
ki kaimata ruwa ta watsa zataji dadi.
Yana zuwa gida yasanar da Mum d’insa
komai, cikin bacin rai takira His
Excellency yana d’auka, tace” ranka
shidad’e! Ya aiki?. Cikin jin dad’i His
Excellency ya amsa. Nan ta sanar masa
da komai, sai da ya jin-jina al’amarin
yace”tun da Baba liman nanan zan sa a
tura 1million sai akai sadaki, 2millions
kuma a had’a kaya akai. Ina dawowa sai
aure kawai. Mumcikin farin ciki
tace”Allah ya ja kwanan mai girma
governor, godiya muke Allah ya tsare
mana kai, Ya amsa da ameen.
Malam ko da ya dawo ransa ya baci,
amma yace”duk hakan baza’a fasa
auren nan ba sai anyi, duk mai hassada
sai dai yayi ya gama. Dr Umar ko kulum
sai yayi sawu 3 a gidan kula ta
musamman ke ba Khadi.
Yau da yazo bayan sun gaisa da malam
ya saida masa “iyayensa zasu zo, za’a
kawo sadaki. Malam yace”Alhamdulilah!
Allah ya kawosu lafiya mungode.
Washe gari Baba liman yazo ya kawo
sadaki, Malam sai da ya razana, kin
karban kud’in yayi yace”gaskiya Malam
sunyi yawa a rage. Baba liman yace”sam
bazan koma da ko si-si ba, mudai fatan
mu Allah ya sanya alkairi. Baban Khadi
ganin Malam ya girmesa, kuma bazai
iya masa musu ba ya sa hannu ya
karb’a.
Yana shiga gida don ya ba ma Gwaggo
haushi yace”Hauwa kawo min taburma
nan kizo kiga ikon Allah. Da sauri
Gwaggo ta fito har tana tun-tub’e, ta
shin fid’a masa tabarma bayan ya zauna
sai taga ya zaro da min kud’i har bunch
biyar, ido Gwaggo ta zaro, “Malam ina
kasamu wanna kud’i?. Murmushi yayi
yace”Hauwa wato zakaran da Allah
yanufa da cara ko ana muzuru ana
shaho sai yayi. “Kuma d’an hakin da
karaina wataran sai ya baka mamaki.
Gwaggo tace”ni dik ban gane hausanka
ba Malam?.
Malam yace”hmm Sadakin Khadi aka
kawo har naira na gugan naira million
d’aya. Wayyo nashiga uku sadaki ina
Malam d’an yankan kai ne ba fa
zaiyuba. Nima sai ka samo ma Bedba
miji, Gwaggo ta sha kwalan Malam, ihu
take tana kuka, tana fad’in ya cuceta.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:

YAYA DA DUKIYA.... 91-100

YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-96~100.
Tana fita suka nufi gida, da gudu ta
shige d’akinta, kuka ta rinka rusa sosai,
Hajiyarta ne ta shigo, tace”Zuly mai ya
sami k’awarki ne?. Zuly tafara bama
labarin komai. Hajiya tanisa
tace”Zulaihat ba ki ba ma kawarki,
shawara mai kyau, tunda Umar baya
sonta, sai ta hak’ura, ko ana son dolene,
kusani a ko da yaushe mace, ita ke jan
kimarta, nikam bazan goyi bayan k’arya
ba. Kunutsu kusan mekukeyi kun fa
girma fa, ae ko irin shigan da kukeyi,
wazai so ku?. Inayi fad’a Abban su
Sakeenah, yace nacika takura masu, ga
irinta nan, nima ina goyon bayan Umar,
matsawan ba canzawa kukayi ba. Kukan
Sakeenat ya karu, sai buga k’afa takeyi,
tana cewa”Hajiya ni baki sona, tunda
bakison abunda nake so, “tsawa ta daka
mata, ke bana son aakarcin banza da
wofi fa, sai da tamusu ba dad’i, tukun ta
bar d’akin.
Dr Umar kuwa lallashin Khadi yayitayi,
Gwaggo ne ta shigo da sallamarta, tun
daga waje an fata rahoto, shiyasa take
fara’a, tana ganin Umar, tace” eehehe
duniya yau taimin dad’i, in dai a kanka
ne, da Khadi naso da dukan tsiya suka
mata, ka wani shigo mana gida d’an
iska, wato karuwanka ne suka kasa
hak’uri suka biyo ka nan?. Ran Umar in
yayi dubu ya baci, don ba abuda yatsana
kaman a danganta shi da mazinaci.
Gwaggo ta zagesu tass shida Khadi, tayi
d’aki, Beebah ko sai basu hak’uri takeyi,
Khadi kam kuka takeyi, kafansa yaja jiki
ba kwari ya bar gidan.
Malam ya na dawowa ya samu labari,
yajima yana tunani daga k’arshe, yace
anya kuwa bazan dakatar, da Umar da
zuwa gidan nan ba?. Haka ya ta sake-
sake, har ya tsayar da amsa ma kansa.
Bayan kwana biyu Umar yazo, tun a
waje suka gaisa da Malam, nan ya fara
ba ma Malam hak’uri, Malam yace”ba
komai ya wuce, amma inaga ka hak’ura
da zuwa kawai, tunda daman ba wata
alaka bace a tsakanin ka da Khadeejat,
cikin firgici ya d’ago, yanaso yayi
magana ya kasa, Malam yajima yana
zargin Umar na son Khadi, amma bai
furta ba, shiyasa yayi hakan don ya
tabbatar. Don zan bada dama ga mai
sonta ya turo magabatan sa, ayi magar
Aurenta kawai. Inaga hakan shine zai
zame mata hutu, Umar duk ya rud’e,
yakasa magana jiki ba kwari, yabar
unguwan, gudu yakeyi Allah ne ya kaisa
gida lafiya, yana zuwa ya tarar da Mum
a falo, gunta ya nufa, ya kwantar da
kansa, a kan cinyanta, sai ga hawaye.
Cikin sanyin murya yace”Mum zan
rasata, Mum ki taimaka min, pls dan
Allah!. Cikin rashin fahimta Mum
tace”wacece zaka rasata?. Ajiyar zuciya
ya sauke, Yace”Mun Khadeejat ce, Mum
tace”kamar yaya zaka rasata?. Nan ya
kwashe labari, ya fad’a ma Mum komai.
Tab lallae Sakeenat bata kyauta ba,
amma ko da Dad d’inaka bai dawo ba
zamuyi waya dole asan abinyi.
A yan kwanakin nan duk Dr Umar ya
rame, hakan yasa Mum, ta sanar da Dad
d’insu, ko da sukayi magana dashi,
yace”bazai samu daman dawuwa, a
satin ba don haka zai sa mataimakinsa,
yaje da kansa, Mum tace” ni a’a ban
yarda ba, kasan Alhaji Bashir baya da
sauki, akan yara , kawai inaga zamu
nimi wani yaje, kuma kaga yanda
yakeson Sakeenat, komai zai iya yi. Dad
yace”shikenan duk yanda kukayi, Mum
ta sanar da Umar komai yayi murna,
sanna yace”shi yanaga a tura Baba
Liman, don yana da halin dattaku. Haka
ko akayi, Baba Liman yaje neman auren
Khadi ma Umar, basu wani samu
Matsala Baban Khadi ba ya amince. Nan
suka zuba kayan mun gani anaso, da
kud’in gaisuwa dubu 2k, Malam yaki
karba yace sunyi yawa, amma Baba
Liman ya dage sai da ya karba. Da
murna yashiga gida, a zuciyar shi, yana
mai cewa tabbas Khadijansa zata huta,
don da alama Umar d’an manyan
mutanene, kuma zai riketa da AMANA.
da murna ya shiga gun Gwaggo, cikin
zak’uwa takaleshi “Malam lafiya naga
sai farin ciki kakeyi?. Hmm kedai bari
kawai, ina cikin farin ciki, mik’omata su
gidan goro da catoons d’in minti yayi,
tare da d’aura mata damin kud’i akai,
ido ta zaro su waje, “Malam wayan nan
kud’in fa da kayan fa?. Cikin murmushi
yace”na Khadijat ne, kud’in aurenta.
Jakar uba! Ina bazai yuba, ina na Beeba
ko Rabee’atu?. To ba a gidan nan za’ayi
wannan abun ba, sai dai ko inda Beeba
ne. Malam yayi dariya yace”Hauwa
kenan wai meysa ba kya boye
hassadanki a fili, ae ni na d’auka Khadi
da Beeba da, Rabee’at, duk d’aya suke a
gunki?. Allah ya sauwake, nawa-nawa
ne. Kuma wannan auren bazai yuwuba,
sai dai ko in zaka kawo na Beeba sai a
had’a. Shikam dariya ta basa, don suk
tagama fita a hayyacinta, ya d’ibi kayan
ya kai d’akinsa. Khadi najinsu amma
duk ta damu da taji wa Malam zai
had’ata aure da shi?.
Malam ne ya shigo d’akinta, ya zauna a
kujera, cikin nutsuwa ya kira sunanta, ta
amsa, sai da yamata nasiha, kamar
yanda ya saba, tukun ya saida mata,
Umar ya kawo kayan ,yagani yana so,
ina fatan kin amince kina sosa?. Shiru
tayi, daga yanayinta ya gane ta amince,
albarka ya samata ya fita.
Washe gari Dr Umar yayi wanka sa, yayi
kyau sosai, sai da yabiya Sahad ya mata
shooping mai yawa, tukun ya nufo
gidan, yaro yasamu ya aika ta fito. Cikin
nutsuwa take takawa, tana sanye da
hijab ash yamata kyau, hannu tasa a
aljihu yana kare mata kalo. Da sallama
ta karaso bayan sun gaisa, yace”gimbiya
Khadeejatu, murmushi tayi yace kali
nan, tana d’ago fuska ya kashe mata ido
d’aya, tare da d’aga mata gira, duk sai
taji kunya ya kamata. Haka sukayi
hiransu a zaure, sai dab zai tafi ya d’ebo
mata, kayan saya mata, godia ta masa
har zata tafi yace”tsaya barin yi
surprising d’inki, murmushi tayi. Yace”
pls close ur eye, ba musu ta rufe, ” miko
hannuki, bata komai ba ta mika masa
tana murmushi, wani zobe ya ciro sai
kyali yakeyi, ya sanya mata a hannu,
nan take hannuta ya d’au kyalu yana
haskawa. Kiss ya kaimta a hannu, sai
sukaji, la ha ila ha illalahu, uhu jama’a
da sauri Gwaggo ta damke su duka. Ta
kwalala jama’a ku kawon d’auki na
kama yan iska yau. Ihu take kamar
mahaukaciya, Khadi ko duk jikinta sai
bari yakeyi, nan take hawaye ya fara
zuba, Umar ko don takaici kasa motsi
yayi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

YAYA DA DUKIYA... 91-95

YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-91~95.
Karfe shidan yamma, jirgin su ya sauka,
acikun garin Abuja. Bata bata lokaci ba,
ta sake shiga jirgin Kano, ko da ta iso,
anyi sallah magriba, ana shirin yin
isha’i, taso yau taje taga yar gidan uban
waye, Dr Umar ke sonta, kuma da me
tafita da shi, da har zai aureta, tabbas
yarinyan sai ta raina kanta, washe gari
da had’a security dinta, wankan kece
raini tayi, ta kira kawarta, Zulaihat
tace”Zuly ki shirya kizo, zaki rakani,
wani karamin unguwa, wai shi Dakata.
Cike da tsokana Zuly tace”kawas mai
zaki dakata acan, nan Sakeenat, ta sanar
mata da komai, Zuly tace”ban minti
kad’an ina zuwa ko ku biyo ku d’auken.
Haka akayi, suka dauketa, cike da rashin
mutunci a fuskokinsu.
Khadi ko wanka tayi, sabi da tasan yau
weekend, Ya Umar d’inta zaizo, tayi
kyau kamar wata amarya. Suna tsakar
gida suna tad’i’ ita da Beebah
kasancewan, Gwaggo ta tafi gidan
kawarta, shiyasa suka sami freedom yau.
Tun daga nesa suke jin, wi wi wi wi,
kukan jiniya alamar, wani babab yazo
unguwan, har sai da aka zo qofar
gidansu, tukun kukan ya tsaya, cikin
mamaki suna jira suji maisu shigowa,
Khadi tace”Beeba kardai police ne suka
zo gidannan?. To wayayi laifi?. Tana
wannan tunani ko taga masu bakaken
kaya, suna shigowa cikin gidan, nan take
hanjin cikinta ya kad’a.
Sai da suka shigo, sun tsatsaya musu,
wasu yan mata ne biyu, su ka danno kai
cikin gidan, kalo d’aya zaka musu ka
gane, sun san bariki, idonsu abud’e
yake, ga fiskansu ta sha man bleaching.
Cikin isa da taunar chewing gum, ta iso
gaban su, sai da suka musu kalon, sama
da kasa, kafi ta juya, ta kare ma gidan
kalo. A tare suka kwashe da dariya, Zuly
tace”kai yayan talakawa, a cikin ku
waye Khadi ko Khadija, shiru ba wanda
ya bada amsa. Cikin zafin rai suka sake
magana, da kyar, Khadi tace” gani nice
Khadi. Sai da suka kaleta sama da kasa,
sai da gaban Sakeenat ya bmfad’i don
sai yanzu ta lura da Khadi, tabbas
yarinyan ta had’u, dole Dr Umar ya
makance a sonta. Daurewa tayi, ta fara
yi ma Khadi, “concrete warning, duk
randa naji ance kin kula Umar sai na
muki rashin mutunci, sai nasa an
d’aureki, tabbas duk halin naka-naka ne,
mai rashin kunya ma wataran yana da
rana. Beebah da Khadi kasa magana
sukayi, Rabee’at dake bacci a d’aki,
hayanayi ya fitar da ita, jin yanda, aketa
zaginsu, dana iyayensu ta karaso da
gudu, ta kalisu Sakeenat, ta sama da
kasa, ta nuna su da yatsa, tace”banza
mai fiskan biri, kin wani sha bleaching,
waye ke?. Da har zakina zagin iyayena,
nan Rabee’at tashiga sauke musu,
kwandon rashin kunya.
Dr Umar yayi wankan sa ya nufo, gidan
su Khadi, tun da ya shigo unguwan ya
fara ganin motoci, har ya iso qofar
gidansu Khadi, nan yaga security, gidan
gwamnati, da sauri ya fito daga mota, ya
kira wani body guard, tambayesa mai ya
faru, nan yake basa bayani, Sakeenat ne
a ciki, da sauri ya shiga gidan, dai-dai
likacin da, Sakeena ta harzuk’o zata
mari Rabee’at da sauri Khadi, ta shiga
tsakanin su, sai jikayi tasss!!, karan
saukan mari a fiskan Khadi, kafin ta
motsa, sai nasojin wasu karan tass!!
Tasss!! Tass!! Gar sau uku, Dr Umar ya
mari Sakeenat. Ya juya ya kali security
d’in, da sauri suka bar cikin gidan. Cikin
fushi ya kali Sakeenat, Yace” kee waya
baki izinin zuwa gidan nan?. Duk randa
na k’ara, ganin k’afarki sai kinji
ajikinki, ki kuma sani Khadeejat ta miki
nisa, itace uwar ‘YA’YA Na, ita nakeso,
itace rayuwa, farinciki na, in part
rayuwata bazatayi dai-dai ba in ita,
banza sakarya, ko ana soyayyan dole
ne?. Nace bana sonki bana sonki, ba
kuma zan soki ba. Cikin b’acin rai yazo,
rik’o hannu Khadi yace”My wife kiyi
hak’uri dan Allah, hannu yasa, ya share
mata hawayenta. Ya rike hannuta, ya
Sakeenat da bakin ciki ya isheta, kaman
ta shid’e a gurin. Yace”kee Sakeenat!
Kinga wannan ta fi minke komai, itace
mahad’an rayuwa ta, tafiki kamun kai,
da nutsuwa, in kin…… Da gudu ta bar
cikin gidan tana kuka, wi-wi da hawaye.
Tabbas yau taja ma kanta raini agaban,
wayanda take takasu son ranta, yau
Umar ya mata haka?. Tana fita mota
tashiga, Zuly ma ta biyota, rake suka bar
unguwan.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

YAYA DA DUKIYA....86-90

’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-86~90.
Sai da yayi musu, sayya mai yawa, ya
nufi Asibiti. Ko da ya shiga, sai da ya
biya office dinsa, ya ajiye wasu files,
kafin ya nufi ,d’akin da su, Khadi suke.
Da sallama ya shiga, suka amsa masa.
Beebah ne “ta gaida shi, cikin
girmamawa ya amsa, “ya tambayeta ya
mai jiki?. “Ba shi amsa da sauki
Alhamdulilah!. Fita tayi ta basu guri, ya
kali Khadi da ke kwance, “ta gaida shi,
cikin muryan, marasa lafiya, “ya amsa
mata, tare da tambayan ya jikinta?. ta
bashi amsa da sauki. Ido ya zuba mata,
har saida tasoma jin kunya, ajiyar
zuciya ya sauke, ya kara lumshe idonsa,
a hankali ya bud’esu, cikin wani salo, da
karya murya, ya kira sunan Khadeejat!!!.
Duk da rashin lafiyan da take fama
dashi, sai da taji, jikinta yamata, wani
iri,”Na’am ta amsa masa cikin siririyan
muryanta. Ya kaleta, yace”Khadeejat!.
Na kasa hak’uri akanki, Khadeejat!. Ki
taimaki zuciyata, da take fama da
azaban sonki, My Khady tun randa, na
fara d’aura idona a kanki, nakamu da
qaunar ki, ki taimaka in samu gurbi, a
cikin zuciyarki. Duk maganan, da yakeyi
Khadi, bata ce komai ba. Sai lumshe
idonta datayi, kamar mai jin bacci, cikin
kasa-kasa da murya, harda d’an
sauk’owa daga kujera, Yace”pls
Khadeejat ki taimaki rayuwata. Tabbas
nasan ina aure ki, a matsayin mata,
kuma uwar ‘YA’YA NA, nasan zasuyi
alfahari dake, a matsayi uwa ta gari.
Khadeejat!. Ki sani duk wani abunda
akeso, mace ta gari ta had’a, kin had’a.
Khadeey na!! I’m deeply in ur love,pla
don’t let me go!! You d joy of my lyf, pls
n pls Khadeey!!, ki samamin matsuguni,
a zuciyarki, ko k’ad’an ne.
Ganin shiru batace komai ba,
Yace”Khadeetaul~Kubrah, in kin amince
pls ko murmushi, kimin in samu sanyi, a
zuciyata. Ganin shiru yasa yanayinsa ya
canza, duk da idonta na rufe, tana iya
ganinsa, amma shi bai lura, da hakan ba.
“Wani lallausan murmushi ta saki, tare
da rufe fuskanta. Ganin haka, ya sauke
ajiyar zuciya, yayi godiya ma Allah. Juya
masa baya tayi, duk yanzu kunyansa, ta
soma ji, ya dad’e yana mata hira, ganin
tana jin kunyarsa, ya ajiye mata waya
tare da mikewa, Yace”yau k’anwata
kunya na takeji, amma badamuwa,
wataran zanyi maganin kunyan nan.
“Ga wannan d’an ajima zamuyi waya,
ya fita abunsa, a waje yayi sallama da
Beebah. Ko da tashi go d’aki, lokacin
Khadi ta mike, sai murmushi take
zubawa, Beebah tace”Addah lafiya
naganki cikin wannan fara’a?, cikin
zumud’i ta labarta ma Beebah, itama
tayi murna sosai,nan suka bud’e, kayan
da yakawo musu, yasha addu’a kam,
suna bud’e na waya, kalo ya koma
kansa, sun yaba da kyan, wayan sosai.
Sai can dare taji wayar na k’ara, ko da
tad’aga wayar kasa d’aukan kiran, duk
sun rasa ma ya’akeyi, Beebata tayi nata
basiran ama ina! Har wayan ta yanke,
sai can dai Khadi tace”tsaya inaga
wannan, ruwan ganyen ne amsa kira, do
d’azu jan ya katse ne. Tana jan ruwan
ganyen, ta tafara jin magana.
Assalamu’alaikum! Wa’alaikumusalamu!
Ta amsa, sai tayi shiru, ”
Khadeejat ya jikin?. “Da sauki
Alhamdulilah!. Hira ya rinka janta dashi,
har sai da yaji, kamar bacci na son
d’aukanta, ya kyaleta.
Kwanan Khadi 7 aka sallameta, tayi fress
kamar batayi rashin lafiya ba, suna
dawo gida, suka samu Gwaggo bata nan,
suka shiga, harda Dr Umar ganin irin
yanayi, d’akin da Khadi take kwana,
ransa ba dad’i ya kira waya, ba’a fi
minti talatin ba, sai ga mota da sabuwar
Katifa, irin manyan nan, da filo da
bargo, aka gyara d’akin fess, ya musu
sallama ya tafi, ko da Malam ya dawo
yayi godiya, ana haka sai ga Gwaggo.
Yau kam ta cika kamar zatayi hakuka,
don ba haka taso ba, taso a fitar da
kayan amma Malam ya hana. Rayuwa
sai tafiya yakeyi, soyayya tsakanin Khadi
da Dr Umar sai abunda ya karu, kulum
suna gaisawa da Ilham, harta sata a
group d’in novel ta yi kawaye yanzu.
Duk inda kake da jama’a, baka rasa yan
gulma, acikin mukaraban, Dr Umar
ansamu wanda ya sanar da Sakeenat, Dr
Umar yana neman wata yarinya, yanzu
haka ana kan shirin magana Aure, nan
take hankalinta ya tashi, bashi ta biyo
jirgi yau ta tazo 9ja.

YAYA DA DUKIYA...81-85

YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-81~85.
Malam sun isa Asibiti, direct office d’in
Dr Abdul sukaje, Don tambayansa, ko
nan aka kawo Khadija, don shi har
yanzu, bai san a ina, Dr Umar yake aiki
ba. Duk da yasan dai, shi likita ne, suna
zuwa suka tarar da Dr Abdul a office,
cikin yanayi damuwa Malam”ya
gaidashi, ya tambayes ya aiki?.
Alhamdulilah!, Malam yace”Dr dan
Allah, ko nan asibitin, aka kawo Khadi?.
Dr Abdul ya amsa masa da eh!. Barin
rakaku d’akin da take. Sai da sukayi
tafiya mai d’an nisa kad’an, kafin suka
shiga, wani Ward mai kyau, kana shiga,
falo zakagani babba, sai gurin da likitoci
ke zama, gefe kum d’akin hutun likitoci
ne. Sai d’akuna da suke jere, gwanin
birgewa, gurin tsab da shi, kamar ba’a
cikin asibiti ba. Kowani d’aki gado
d’ayane a ciki, sai yar loka da ke gefe,
Malam suka tura, qofar d’akin da
sallamansu. Dr Umar ne zaune ya zabga
tagumin gaban Khadi, sam bai masan
sun shigoba, suka sake mai-maita
sallama, amma shiru, Dr Abdul ne ya isa
gunsa da sauri ya dafasa, yace”my
friend, cikin razana ya d’ago, sai a
lokacin yaga Malam, duk kunya ta
rufesa.
Mik’ewa yayi da sauri, yana musu,
sannu da zuwa. Kalo d’aya Malam yayi
ma Khadi, yaji wani mugun tausayinta,
ya kamasa, tambayan kamsa yayi anya
bayi da laifi, shima acikin cutar da
Khadi, da Gwaggo takeyi?. Idonsa ne ya
ciko da kwala, bakin gadon yaje, ya rike
hannuta, cikin muryan damuwa,
Yace”Khadijatu kiyafr min, duk nine
silan saki, cikin wannan damuwar.
Tabbas Hauwa watarana sai tayi
nadama, mai d’umbin yawa, Allah ya
miki Albarka, ya Allah kajikan Adamu.
Duk wanda suke gurin saida jikinsu yayi
sanyi, Beeba kam kuka takeyi sosai.
Malam ya juya ya kali, Dr Umar
yace”Umaru na rasa, da wani irin,
kalma zan gode maka. Tabbas ka taimaki
Khadijatu iya taimako, Allah ya bamu,
abunda zamu saka maka dashi.Allah ya
maku Albarka
Cikin zuciyan Dr Umar yace”abida
zaumin kad’ai kubani Khadijat, don
zuciyata, takamu da azaban sonta.
Gwaggo da ke gida, sai fatan take, “Allah
yasa adawo, da gawan Khadi. Na tsani
ganinta, kamar mayya, komai zakamata
bata zuciya. Mtsss ina da daga nan,
tashiga uwa duniya, in huta da
fitinaniyan, yarinyannan.
Ko da taji Beebah tabi Malam, sun tafi
asibiti, bakaramin haushi tajiba.
Tunanin kalan, rashin mutuncin da zan
masu.
Kwanan su Khadi, biyu a Asibiti, Dr
Umar shi ke d’awainiya da su. Kulum
yana hanyan Asibiti, yana tashi daga
aiki bayan ya duba Khadi, shagon waya
ya zarce, yasaya mata, iPhone 7, wayar
ta had’u. Gida yanufa, yana zuwa, yayi
wanka, ya fito dining, Iham ce tazo
tazauna a gefensa, tana masa surutu, can
idonta ya kyalo waya maroon, tace”bros
wannan fa?. Tare da kai hannuta ta
d’auka, “bros wayan tayi kyau, bai
kaleta ba Yace”na Khadiyat ne, ihu tasa
tare da cewa”wooow wayan tayi kyau.
Barin samata number, nan harda
WhatsApp, ta bud’e mata. Sai da yagama
tukun ya amshi wayan yafita.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

YAYA DA DUKIYA... 76-80

YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-76~80.
Da sauri ya tareta, ta fad’a hannusa,
sunanta yakira, Khadijat! Khadijat
Khadijat… Pls ki tashi, kar ki tafi ki
barni lokacin dana ke bukatarki, kene
farin cikina. Pls Khadijat, yana jijigata,
amma sam ko motsi batayi, Dr Umar ya
fita a hayyacinsa, sai sam batu yakeyi,
Gwaggo ko wani ruwan sanyi, tasake
d’ebowa bata tsaya, wata-wata ba, ta
k’wara ma Dr Umar. Duk da na da lafiya
sai da ya razana, ajiyar zuciya ya sauke,
nan take ya dawo cikin hayyacinsa,
hannu sa ya kala, da sauri ya d’auketa,
cikin mota ya sanya ta. Da gudu yabar
unguwan. Asibitin Murtala ya wuce,
yana zuwa ya d’auketa a hannu,
Emergency yayi da ita. Kasancewar shi
duty safe ke dashi, Dr Abdul ke duty
kwana. Da sauri ya d’aga waya ya
kirashi, “Dr Abdul dan Allah kazo
Emergency, Khadija tace bata da lafiya,
kazo ka taimka min, muryansa kaman
zaiyi kuka, duk ya rud’a Dr Abdul, don
bai kuma taba jin, Dr Umar cikin
wannan, yanayin ba. Dr Abdul
yace”Friend wacece Khadija?.cikin fushi
yace”Malam in zakazo to in bazaka zo
nakira, DR James, kashe wayan yayi,
yafara kiran Dr Jame kenan, Dr Abdul ya
turo qofar ya shigo. Da sauri yayi kanta,
yana ganin Khadi ce, mamaki ya cikasa,
tambayoyi yafara yi makansa,” daman
Umar yasan Khadi ne?.
“To mai yasa yarinka min tambayoyi
akanta?.
“Ta ya’akayi tazama Khadijansa?.
Maganan Dr Umar ne ya dawo da shi,
daga dogon tunanin daya shiga.
Dr Umar Yace”kai Malam, lafiya kake
mata, irin wan kalon?. Da sauri yazo ya
kareta, cikin kishi da jin haushi, yake
maganan. Dr Abdul bai cemasa uffan ba,
cikin hanzari yasoma dubata, daman
yariga yasan matsalanta, cikin ikon
Allah, ansamu numfashin ta, ya dawo
dai-dai. Sai dai bata farka ba, sun mata
aluran baci, don ta samu hutu.
Special room aka kaita, don hutawa ita
kad’aine a d’akin. Dr Umar ya zauna, a
bakin gadon ya zuba mata ido, ko
kyaftawa ba yayi. Ji yake kaman ya
k’arba mata ciwon, Dr Abdul ne ya
shigo, yace”Ya mai jiki?. Da sauki ya
bashi amsa. “Allah ya k’ara sauki. “In ka
gama kasameni a office d’ina. Ok! Dr
Abdul ya fita, office d’insa ya koma, ya
zauna cike da tambayoyi, a fuskansa. Dr
Umar sai daya kai, kusan kamar 1hrs,
kafin ya kira nurse, yace”ta kulamasa,
da patient d’insa.
Da sallama ya shiga office d’in Dr Abdul,
bayan ya zauna ne, Dr Abdul
Yace”friend ina kasamu Khadi?. Ko
dama ka santa tun-tuni, Dr Umar yace”
kai ka santa ne?. Dr Abdul ya d’aga masa
kai alamar eh!. Ajiyan zuciya Dr Umar
yayi, nan ya kwashe labari, tunga randa
ya fara ganinta, har yanzu, dayake fama
da azaban sonta. Sai da Dr Abdul ya
jijina kai, yace”Allah mai iko, to ae itace
Khadijan, da ranan kaji ana case akanta.
Cikin mamaki Dr Umar yace” mai kace
ne ban fahimta ba. Nan Dr Abdul
yabashi labarinta, iya yanda ya sani.
Umar ya tausaya mata ba kad’an ba,
wani Sonta da Qaunarta, suka k’ara
shigansa. Cikin tsokana Dr Abdul yace”
friend amma gaskiya, ka cika kishi,
kawai don ina mata kalon sani, amma
kawani tare, dariya Dr Umar yamasa,
tare da kai masa dukan wasa.
Malam dawowansa, daga kasuwa kenan,
aka basa labarin, abunda ya faru bai iya
shiga gidan ba, ya juya zai tafi kenan,
yaga Beeba ta fito, duk ta rud’e hijab ma
bai-bai tasa. Da sauri ta bisa, Napep ya
tsara musu, suka nufi Asibitin Murtala.
Zuciyan Malam sai tafasa yakeyi, yana
tunanin wani kalan hukunci, zai yanke
ma Gwaggo. Don abuntan yayi yawa,”to
wai mai Khadi ta tsare mata a
rayuwanta ne?. Da takeson ganin
bayanta, tabbas zai Aura da Khadi, don
ta huta da bala’in Gwaggo.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:

'YA'YA DA DUKIYA.... 71-75

YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-71~75.
Khadi kulum tana cikin k’unci, Gwaggo
ta sata a gaba, baran in taga, Malam ya
fita kasuwa. Gashi Dr Umar ya kwana
biyu bai zoba, d’inki ma, tabar zuwa
sabida bala’in Gwaggo, wai sai Malam ya
saka su duka, don su Beeba su samu
suma mai saya musu kaya. Malam ko
yace”bata isa ba, tayi k’ad’an ta gindaya
mishi sharad’i yabi. Tunda tun farko,
Khadi ne tafara cewa tana so, dan haka
ba zaisasu ba. Zaban tayar musu da
hankali yasa Khadi ta samu Malam tace”
Baba bana jin dad’i zan d’an huta da
zuwa aiki, kafin wata sati, Tukun ya
hak’ura.
Dr Umar ko, bai da tunani da yawuce na
Khadijat, so ya kemata, wanda shi
kanshi, bazai iya auna shi, a mizani ba.
Masu karatu zamu so musan,
WAYE DR UMAR?
Umar Adam Naira, shine cikaken
sunansa, d’a, d’aya tilo girin Adam
Naira. Adam naira haifafen d’an Kano
ne, nan yayi karatunsa, har ya girma, ya
Auri maransa Maryama, sun dade da
aure, Allah bai basu haihuwa ba, sai
daga baya Allah ya azurta su da
haihuwan Umar, wanda yaci sunan
Baban Mum d’insa, bayan shekaru da
yawa, ta haifi Ilham, wacce itace auta, a
yamzu haka. Alhaji Adam Naira yarike
muk’amai, na gwamnati da dama.
Wanda yanzu haka shine gwamnan
Kano State mai ci. Ya kasance mutum ne
mai kwatanta gaskiya da adalci, hakan
yasa al’uman garin Kano ta Dabo suke
sonsa. Tunda Umar ya taso, shi bamai
son yawan, hayaniya bane, sannan bai
kula yan’mata,sai wata yarinya, Sakina
da ta makalemasa, sam bata cikin
tsarinsa, don bata da kamun kai,
yar’gidan, matai makin governor ne,
gata da rashin kunya, shiyasa basa shiri.
Yanzuma saukin da yasamu, ya dawo
yasamu sun fita waje, ita da Mum d’inta.
Iyayensa burinsu shine, yayi aure amma
baya kula yan’mata. Tun randa ya had’u
da Khadi, tunda yasanar da Mum d’insa,
da murna ta, tasanar da His Excellency.
Yayi farinciki ba kad’an ba. Yace” yana
dawowa zasu samu iyayen yarinyan, ayi
magana a sanya rana.wanna shine
labarin Umar a takaice.
Dr Umar zaune yau, sai tunanin
Khadijat, da ya damesa.
Key mutarsa ya d’auka, yana fitowa
securitys, suka fara gaidasa, da gudu
suka bud’e masa, k’ofar motan yashiga,
gida ya nufa yayi wanka, dun zuwa gun
Khadi. Yayi kyau sosai, ya shiga mota shi
kad’ai batare da security’s ba, ya nufi
gidan.
Khadi ko tunda ta tashi, tashi tana son
yin wanka, kayan da Dr Umar ya kawo
mata. ta d’auko wani less, mai kyau
purple da duwatsu farare a jiki. Tayi
kwaliya sosai, ta kuma yi kyau.
Kasancewan yanayi gari, da sanyi, gun
sai yayi, bada yanayi mai kayatarwa.
Gwaggo ta shiga makwabta, sai zuba
take musu. Yaro ne yashigo”wai ana
salama, da Khadijat inji Umar.
Tace”kace ina zuwa. Yana fita ta d’auko
hijab d’inta fari tasa, bakaramin kyau
tayi ba. Cikin nutsuwa ta fito, tunda
Umar ya hangota, zuciyar sa sai
harbawa, ido ya k’ura mata.
Gwaggo da tafito daga, gidan su abula,
ganin Umar acikin k’atuwar mota, nan
zuciyarta ya fara tafarfasa. Yau mai
zanyi ma Khadi na huce?. Wata zuciya
tace”kawai ki d’auko wuka ki burma
mata. Mtss a’a za’a kamani, can shaidan
ya tuna mata, kawai ki shek’a mata
ruwan sanyi, tunda bata so. Da sauri ta
koma gidan Abula, tace”dan Allah samin
ruwan a fridge d’inki. Sam Abula bata
kawo komai ba, ta iba mata, a karami
roban plastic. Da sauri tayi gida, ta k’ara
dana randa, kamar wata mahauk’aciya
ta fito.
Dr Umar ya shagala, da kalon Khadi,
itako tana wasa, da yan’yatsun hannuta.
Sai jin shaaa… sukayi, take idon Khadi
ya kafe, numfashinta ya d’auke, ta tafi
luuuuu zata fad’i kasa. Da sauri Dr Umar
ya fito, yana kiran sunanta, tareta yayi
ta fad’i a hannusa yana jijigata, amma
sam bata ko motsi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺗﻠﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

'YA'YA DA DUKIYA.... 71-75

YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-71~75.
Khadi kulum tana cikin k’unci, Gwaggo
ta sata a gaba, baran in taga, Malam ya
fita kasuwa. Gashi Dr Umar ya kwana
biyu bai zoba, d’inki ma, tabar zuwa
sabida bala’in Gwaggo, wai sai Malam ya
saka su duka, don su Beeba su samu
suma mai saya musu kaya. Malam ko
yace”bata isa ba, tayi k’ad’an ta gindaya
mishi sharad’i yabi. Tunda tun farko,
Khadi ne tafara cewa tana so, dan haka
ba zaisasu ba. Zaban tayar musu da
hankali yasa Khadi ta samu Malam tace”
Baba bana jin dad’i zan d’an huta da
zuwa aiki, kafin wata sati, Tukun ya
hak’ura.
Dr Umar ko, bai da tunani da yawuce na
Khadijat, so ya kemata, wanda shi
kanshi, bazai iya auna shi, a mizani ba.
Masu karatu zamu so musan,
WAYE DR UMAR?
Umar Adam Naira, shine cikaken
sunansa, d’a, d’aya tilo girin Adam
Naira. Adam naira haifafen d’an Kano
ne, nan yayi karatunsa, har ya girma, ya
Auri maransa Maryama, sun dade da
aure, Allah bai basu haihuwa ba, sai
daga baya Allah ya azurta su da
haihuwan Umar, wanda yaci sunan
Baban Mum d’insa, bayan shekaru da
yawa, ta haifi Ilham, wacce itace auta, a
yamzu haka. Alhaji Adam Naira yarike
muk’amai, na gwamnati da dama.
Wanda yanzu haka shine gwamnan
Kano State mai ci. Ya kasance mutum ne
mai kwatanta gaskiya da adalci, hakan
yasa al’uman garin Kano ta Dabo suke
sonsa. Tunda Umar ya taso, shi bamai
son yawan, hayaniya bane, sannan bai
kula yan’mata,sai wata yarinya, Sakina
da ta makalemasa, sam bata cikin
tsarinsa, don bata da kamun kai,
yar’gidan, matai makin governor ne,
gata da rashin kunya, shiyasa basa shiri.
Yanzuma saukin da yasamu, ya dawo
yasamu sun fita waje, ita da Mum d’inta.
Iyayensa burinsu shine, yayi aure amma
baya kula yan’mata. Tun randa ya had’u
da Khadi, tunda yasanar da Mum d’insa,
da murna ta, tasanar da His Excellency.
Yayi farinciki ba kad’an ba. Yace” yana
dawowa zasu samu iyayen yarinyan, ayi
magana a sanya rana.wanna shine
labarin Umar a takaice.
Dr Umar zaune yau, sai tunanin
Khadijat, da ya damesa.
Key mutarsa ya d’auka, yana fitowa
securitys, suka fara gaidasa, da gudu
suka bud’e masa, k’ofar motan yashiga,
gida ya nufa yayi wanka, dun zuwa gun
Khadi. Yayi kyau sosai, ya shiga mota shi
kad’ai batare da security’s ba, ya nufi
gidan.
Khadi ko tunda ta tashi, tashi tana son
yin wanka, kayan da Dr Umar ya kawo
mata. ta d’auko wani less, mai kyau
purple da duwatsu farare a jiki. Tayi
kwaliya sosai, ta kuma yi kyau.
Kasancewan yanayi gari, da sanyi, gun
sai yayi, bada yanayi mai kayatarwa.
Gwaggo ta shiga makwabta, sai zuba
take musu. Yaro ne yashigo”wai ana
salama, da Khadijat inji Umar.
Tace”kace ina zuwa. Yana fita ta d’auko
hijab d’inta fari tasa, bakaramin kyau
tayi ba. Cikin nutsuwa ta fito, tunda
Umar ya hangota, zuciyar sa sai
harbawa, ido ya k’ura mata.
Gwaggo da tafito daga, gidan su abula,
ganin Umar acikin k’atuwar mota, nan
zuciyarta ya fara tafarfasa. Yau mai
zanyi ma Khadi na huce?. Wata zuciya
tace”kawai ki d’auko wuka ki burma
mata. Mtss a’a za’a kamani, can shaidan
ya tuna mata, kawai ki shek’a mata
ruwan sanyi, tunda bata so. Da sauri ta
koma gidan Abula, tace”dan Allah samin
ruwan a fridge d’inki. Sam Abula bata
kawo komai ba, ta iba mata, a karami
roban plastic. Da sauri tayi gida, ta k’ara
dana randa, kamar wata mahauk’aciya
ta fito.
Dr Umar ya shagala, da kalon Khadi,
itako tana wasa, da yan’yatsun hannuta.
Sai jin shaaa… sukayi, take idon Khadi
ya kafe, numfashinta ya d’auke, ta tafi
luuuuu zata fad’i kasa. Da sauri Dr Umar
ya fito, yana kiran sunanta, tareta yayi
ta fad’i a hannusa yana jijigata, amma
sam bata ko motsi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺗﻠﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ

Popular Posts

 
]]>All content on thisblog are copyright protected and cannot be reproduced on other websites without permission.