New Post

Wednesday, 1 March 2017

BAZATA PG 28

BAZATA 
                By
©Rash Kardam 
    28                  
Cak ya dauketa, ya haura da ita steps din, nan kaji hall ya dauka da ihu da sowa, sai da yaje kujerun da aka tana dar musu kafin ya ajiyeta ya zauna, gsky amare sunyi kyau, ko Rash  sun burgeni, sannu a hankali aka soma guda narda biki, nan aka bukaci amarya da ango su fito fili, hannu ya rike tare da janyota jikinsa suka sauka a hankali, Jiddah kam kunya duk ya isheta, DJ ya sake kida, nan ghali ya soma takawa jiddah kam tana tsaye ganin bata da niyar rawa, ya kama kugunta nan suka soma rawa, hall ne ya dauka da ihu, nan aka soma musu liki, feenat da Samar suka sauko, sai Marsal da Anwar, Sophia da Aslam sai kuma Nuceey da Aminu, abun sai wanda ya gani don sun matukar burgewa, sosai da sosai, liki kam sun sha, masoya sun taka sosai, sai 11:00 suka gama dinner, daga nan aka fito,
ghali da jiddah suka nufi gdan su, kawaye aka mayar dasu gdajen su, gsky gidan jiddah ya tsaru bazan iya kwatanta muku ba, Abba sunyi kokari, bayan Angwaye sun rakasu suka musu Adu’ah da fatan Alkairi, bayan fitarsu ghali ya umarci Jiddah da tayi alwala, suyi sallah, dakinsa ya nufa, wanka tayi kafin ta daura Alwala ta fito batayi wani kwaliya ba tasaka dogon riga da hijab don yin Sallah, shima dai wankan yayi yasanya jallabiya, yasameta, bayan sun idar da sallah yama yan tambayoyi game da Addini ta bashi amsa, Adu’ah niman zaman lfy da zuri’ah ta gari ya musu, tana amsawa da Ameen, bayan sun gama ya dauko musu kaji da fresh milk jiddah taci tace aa yace ta karba taci taki, jalabiyarsa ya cire ya rage daga shi sai gajeren wando da best, duk kunya ta ishi jiddah, hannu yasa ya zare hijab dinta, ta sunkuyar da kanta, kasa yasa abakinsa ya yaga sai da ya dan tauna kafin ya matso kusa da ita ya janyota sai da ta kwata ajikinsa kafin yasa mata abaki kin budewa tayi shiko bakinsan yaringa turawa nata dole yasa ta karba, haka yayita mata sai da ya tabbatar ta koshi kafin shima ya ci bayan sun gama ya kwashe kayan ya kai kitchen, yana zuwa ya ganta inda ya barta, daukanta yayi zuwa kan gado wutar :idea:dakin ya kashe, a hankali ya soma rabata da kayan jukinta nan fa ta rike tasoma bashi hakuri cikin rada yake cemata haba my Jiddah meyasa kike son hanani abunda Allah ya halasta min ko so kike Mala’iku su tsine miki har wayewan gari, kai ta girgiza alamar aaa, rigar ya cire mata sannu a hankali ya rabata da  jiddah sai boye jikinta take, wasani yasoma mata, wanda yasa jikinta mutuwa, nikam ganin abun yafi karfin gulmana    yasa na ja musu kofa na fito sai da safe in leko 

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts