New Post

Wednesday, 1 March 2017

BAZATA PG 29

BAZATA 
                By
©Rash Kardam 
   29                   
Ghali bai saurara ma jiddah ba sai asuba, yau ya mayar da jiddah cikakiyar mace, Albarka kam yau tasha shi, roka  roka  sambatu kam ba’a magana don nikam na dauka ghali ya zautu ne   tsaban Santi yau ghali harda kyautar gida  Ma jiddah    da asuba taimaka mata yayi ta gyara jikinta bayan yaje Masalaci yayi sallah ya dawo itama tayi nata kwanciya suka sakeyi sai goma suka farka lokacin an kawo musu breakfast, wanka sukayi kafin suka karya tayi kwaliyarta cikin atamfanta brown da ratsin silver colour tayi kyau sosai da yamma nuceey sukazo da Sophia nan sukayita sokanarta, hira sukayi sosai sai alokacin sophia ke ba ma jiddah lbr sun hade da Aslam fa Nuceey kuma da Aminu, jiddah tayi murna sosai, sai magriba, suka mata sallama don Nuceey washe gari zasu koma kaya ta hada musu sosai kafin suka tafi
Jiddah sai da satiyi 2 weeks suna cin amarci kafin ghali ya dau hutu suka soma shirin komawa UK don ta karasa karatunta, sai da sukayi sallama masu Abba da gdansu ghali kafin suka dau hanya, ko da suka isa Uk rayuwansu mai dadi cike da kulawa sukayi satinaa biyu ya dawo 9ja.
Nuceey kuwa soyayya tayi karfi tsakaninta da prof har iyaye sunshiga ciki.
Haka sophia da Aslam bikinsu yanzu Saura 3 month soyayyan  su suke sha sosai abun gwanin burgewa,
Jiddah da kuwa ta kara kyau da kiba ga haske, ghali duk karshen wata tana kawo mata ziyara, kamar kulum yanda ya saba yau ma yazo hutun karshen wata, da murna ta tarbesa ta masa duk abunda tasa ba, abinci suke ci cikin kulawa da kaunar juna, Amai ne ya taso ma jidda da sauri tayi toilet, sosai tayi amai wanda ya galabaitar da ita, jikinta ba kwari ghali ne ya gyara gurin kafin ya kamota suka dawo daki ta canza mata kaya suka nufi asibiti, bayan yan gwaje2 da akayi likita ke shai da mu tana dauke da juna na wata3 murna gurin ghali da jiddah ba’a magana haka suka dawo gida yayi ta ririta ta, bayan yagama weekend dinsa zai koma yace ta kula da kanta sosai ga exams ya kusa, ta raka shi har Airport saidata ga jirginsu ya tashi ta dawo, haka sukayita karatu su batan wata daya suka soma rubuta final exams dinsu wata daya sukayi suka gama lokacin cikinta na 6 months, suna dawuwa 9ja suka soma bikin su Sophia da Nuceey haja akayi biki tana da ciki, ga cikin yayi girma2 duk wanda ya ganta sai yace jiddah kodai 2 zaki haifa kamar bacikin fari ba yayi gima sosai, sunyi biki lfy an kai sophia Abuja yayin da Nuceey aka kawota bauchi, haka rayuwa tayita tafiya,
Feenat ta haifi yarta kyakyawa mai kama da ita, yarinyan taci Sunan Hameedah,
Marsal kuwa namiji taifa aka sanya masa Dalhat yaran ga kyau haka rayuwa tayita tafiya.
Yau Alhamis jiddah ta tashi da matsanacin ciwo mara, ghali duk ya rude, kasa mata komai yayi ya dauke ta sai asibiti, basu dade da zuwa ba Jiddah ta haifo yan biyuta mace da namiji, kan kace me asibiti yacika da yan uwa, da yamma aka sallamesu, haka sukayita shirin suna ghali yasai kaya kamar na hauka, ranan suna Saniya  ya naka da rago  yara sunci sunan Amatulhaleem da kuma Abdulhaleem, anyi shagali sosai, kowa ya watse haka rayuwa yaci gaba da wakana, cikin jin dadi da kulawa.
Kwanaki sunja yanzu yaranta sunyi wayo sosai.

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts